< Judges 3 >

1 These are the nations which the Lord left, so that by them he might instruct Israel and all who had not known the wars of the Canaanites,
Waɗannan su ne al’umman da Ubangiji ya bari don yă gwada duk waɗannan Isra’ilawan da ba su san yaƙi a Kan’ana ba
2 so that afterward their sons might learn to contend with their enemies, and to have a willingness to do battle:
(ya yi haka ne domin yă koya wa zuriyar Isra’ilawa waɗanda ba su taɓa yin yaƙi a dā ba),
3 the five princes of the Philistines, and all the Canaanites, and the Sidonians, and the Hivites who were living on Mount Lebanon, from Mount Baal-Hermon as far as the entrance to Hamath.
sarakuna biyar na Filistiyawa, dukan Kan’aniyawa, Sidoniyawa, da kuma Hiwiyawan da suke zaune a duwatsun Lebanon daga Dutsen Ba’al-Hermon zuwa Lebo Hamat.
4 And he left them, so that by them he might test Israel, as to whether or not they would listen to the commandments of the Lord, which he instructed to their fathers by the hand of Moses.
An bar su domin su gwada Isra’ilawa a ga ko za su yi biyayya da umarnin Ubangiji, wanda ya ba wa kakanninsu ta wurin Musa.
5 And so, the sons of Israel lived in the midst of the Canaanite, and the Hittite, and the Amorite, and the Perizzite, and the Hivite, and the Jebusite.
Isra’ilawa suka zauna tare da Kan’aniyawa da Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa.
6 And they took their daughters as wives, and they gave their own daughters to their sons, and they served their gods.
Suka auri’ya’yansu mata, su ma suka bar’ya’yansu maza suka auri’ya’yansu mata, suka kuma yi wa gumakansu sujada.
7 And they did evil in the sight of the Lord, and they forgot their God, while serving the Baals and Ashtaroth.
Isra’ilawa suka aikata mugunta a gaban Ubangiji; suka manta da Ubangiji Allahnsu suka kuma bauta wa Ba’al da Ashera.
8 And the Lord, having become angry with Israel, delivered them into the hands of Cushan-Rishathaim, the king of Mesopotamia, and they served him for eight years.
Fushin Ubangiji kuwa ya yi ƙuna a kan Isra’ila har ya sayar da su ga Kushan-Rishatayim sarkin Aram-Naharayim, a wurinsa ne Isra’ilawa suka zama bayi shekara takwas.
9 And they cried out to the Lord, who raised up for them a savior, and he freed them, namely, Othniel, the son of Kenaz, a younger brother of Caleb.
Amma da suka yi kuka ga Ubangiji, sai ya tad musu da mai ceto, Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb wanda ya cece su.
10 And the Spirit of the Lord was in him, and he judged Israel. And he went out to fight, and the Lord delivered Cushan-Rishathaim, the king of Syria, and he overwhelmed him.
Ruhun Ubangiji ya sauko masa, domin yă zama mahukuncin Isra’ila yă kuma je yaƙi. Ubangiji ya bayar da Kushan-Rishatayim sarkin Aram a hannun Otniyel, ya kuwa sha ƙarfinsa.
11 And the land was quiet for forty years. And Othniel, the son of Kenaz, died.
Saboda haka ƙasar ta zauna da lafiya shekara arba’in har sai da Otniyel ɗan Kenaz ya rasu.
12 Then the sons of Israel resumed doing evil in the sight of the Lord, who strengthened Eglon, the king of Moab, against them because they did evil in his sight.
Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda sun aikata wannan mugunta sai Ubangiji ya ba wa Eglon sarkin Mowab ƙarfi a kan Isra’ila.
13 And he joined to him the sons of Ammon and the sons of Amalek. And he went forth and struck Israel, and he possessed the City of Palms.
Da ya sami Ammonawa da Amalekawa suka haɗa hannu tare, sai Eglon ya tafi ya auka wa Isra’ila, suka ƙwace Birnin Dabino.
14 And the sons of Israel served Eglon, the king of Moab, for eighteen years.
Isra’ilawa suka zama bayin Eglon sarkin Mowab shekara goma sha takwas.
15 And afterward, they cried out to the Lord, who raised up for them a savior, called Ehud, the son of Gera, the son of Benjamin, who used either hand as well as the right hand. And the sons of Israel sent gifts to Eglon, the king of Moab, by him.
Isra’ilawa suka sāke yin kuka ga Ubangiji, ya kuwa ba su mai ceto, Ehud, wani bahago, ɗan Gera daga kabilar Benyamin. Isra’ilawa suka aike shi da haraji wurin Eglon sarkin Mowab.
16 And he made for himself a two-edged sword, having a handle, reaching to the middle, the length of the palm of a hand. And he was girded with it under his cloak, on the right thigh.
To, Ehud ya riga ya ƙera takobi mai kaifi biyu mai tsawo wajen kamu ɗaya da rabi, wanda ya yi ɗamara da shi a cinyarsa ta dama ƙarƙashin rigarsa.
17 And he offered the gifts to Eglon, the king of Moab. Now Eglon was exceedingly fat.
Ya kai wa Eglon sarkin Mowab harajin, wanda yake mai ƙiba ne.
18 And when he had presented the gifts to him, he followed out his companions, who had arrived with him.
Bayan Ehud ya ba da harajin, sai ya sallame mutanen da suka ɗauko harajin.
19 And then, returning from Gilgal where the idols were, he said to the king, “I have a secret word for you, O king.” And he ordered silence. And when all those who were around him had departed,
A wajen gumaka kusa da Gilgal, shi kansa ya juya ya koma ya ce, “Ranka yă daɗe, ina da saƙo na asiri dominka.” Sarkin ya ce, “Ku ba mu wuri!” Sai dukan fadawansa suka fita.
20 Ehud entered to him. Now he was sitting alone in a summer upper room. And he said, “I have a word from God to you.” And immediately he rose up from his throne.
Sai Ehud ya matso yayinda shi kuwa yake zaune shi kaɗai a ɗakin sama mai sanyi a fadansa ya ce, “Ina da saƙo daga wurin Allah dominka.” Sarki ya tashi daga kujerarsa,
21 And Ehud extended his left hand, and he took the dagger from his right thigh. And he thrust it into his abdomen
Ehud ya kai hannun hagunsa, ya zaro takobi daga cinyar ƙafar damansa ya soki sarki a ciki.
22 so strongly that the handle followed the blade into the wound, and was enclosed by the great amount of fat. Neither did he withdraw the sword. Instead, he left it in the body just as he had struck with it. And immediately, by the private parts of nature, the filth of the bowels went out.
Har ƙotar ma ta shige ciki, takobin kuma ya fito ta bayansa. Ehud bai zare takobin ba, kitse kuwa ya rufe shi.
23 Then Ehud carefully closed the doors of the upper room. And securing the bars,
Sa’an nan Ehud ya fita daga shirayin; ya rufe ƙofar ɗakin saman, ya kuma kulle su.
24 he departed by a back exit. And the servants of the king, entering, saw that the doors of the upper room were closed, and they said, “Perhaps he is emptying his bowels in the summer room.”
Bayan da ya tafi, bayin sarki suka zo suka tarar duk ƙofofin ɗakin sama suna kulle, suka ce, “Wataƙila yana bayan gari ne a ɗakin ciki.”
25 And after waiting a long time, until they were embarrassed, and seeing that no one opened the door, they took the key, and opening it, they found their lord lying dead on the ground.
Suka yi ta jira har suka gaji. Da suka ga dai bai buɗe ƙofar ba, sai suka ɗauki mabuɗi, suka buɗe. Sai ga shugabansu a ƙasa matacce.
26 But Ehud, while they were in confusion, escaped and passed by the place of the idols, from which he had returned. And he arrived at Seirath.
Yayinda suke fama jira, Ehud ya riga ya yi gaba. Ya bi ta wajen gumaka zuwa Seyira.
27 And immediately he sounded the trumpet on Mount Ephraim. And the sons of Israel descended with him, he himself advancing at the front.
Da ya iso can, sai ya busa ƙaho a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuma suka gangaro tare da shi daga tuddai, shi kuwa yana jagorarsu.
28 And he said to them: “Follow me. For the Lord has delivered our enemies, the Moabites, into our hands.” And they descended after him, and they occupied the fords of the Jordan, which cross over to Moab. And they did not permit anyone to cross.
Ya umarce su ya ce, “Ku bi ni, gama Ubangiji ya ba Mowab abokin gābanku a hannunku.” Haka suka gangaro tare da shi suna mallaki mashigin Urdun da ta shiga zuwa Mowab, ba su yarda wani ya haye ba.
29 And so, they struck down the Moabites at that time, about ten thousand, all strong and robust men. None of them were able to escape.
A lokacin sun kashe mutanen Mowab dubu goma, dukansu jarumawa da masu ji da ƙarfi; ba ko ɗaya da ya tsira.
30 And Moab was humbled in that day under the hand of Israel. And the land was quiet for eighty years.
A wannan rana aka mai da Mowab bayin Isra’ila, ƙasar kuwa ta sami zaman lafiya shekara takwas.
31 After him, there was Shamgar, the son of Anath, who struck down six hundred men of the Philistines with a plowshare. And he also defended Israel.
Bayan Ehud, sai Shamgar ɗan Anat, wanda ya karkashe Filistiyawa ɗari shida da sandar korar shanun noma, shi ma ya ceci Isra’ila.

< Judges 3 >