< Joshua 8 >

1 Then the Lord said to Joshua: “You should not fear, and you should not dread. Take with you the entire multitude of fighters, and rising up, ascend to the town of Ai. Behold, I have delivered into your hand its king and people, and the city and the land.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoro; kada ka karaya. Ka ɗauki dukan sojojin ku kai wa Ai hari, gama na ba ka nasara a kan sarkin Ai, mutanensa, birninsa da kuma ƙasarsa.
2 And you shall do to the city of Ai, and to its king, just as you did to Jericho, and to its king. Yet truly, the spoils, and all the living things, you shall plunder for yourselves. Set an ambush against the city behind it.”
Za ku yi wa Ai yadda kuka yi wa Yeriko da sarkinta, sai dai za ku kwashe ganima da dabbobinta su zama naku. Ku yi kwanto a bayan birnin.”
3 And Joshua rose up, and the entire army of warriors with him, so that they might ascend against Ai. And he sent thirty thousand elect strong men in the night.
Yoshuwa da dukan sojojin suka fita su kai wa Ai hari. Sai ya zaɓi sojojinsa waɗanda suka fi saura duka iya yaƙi guda dubu talatin, ya tura su da dad dare
4 And he instructed them, saying: “Set an ambush behind the city. You shall withdraw not far away, and let everyone be prepared.
ya ba su umarni ya ce, “Ku ji da kyau, za ku yi kwanto a bayan birnin, kada ku yi nisa da birnin. Kowannenku yă kasance a faɗake.
5 But I and the remainder of the multitude that is with me will approach from the opposite side of the city. And when they come out against us, we will flee and turn our backs, just as we did before,
Ni da waɗanda suke tare da ni za mu nufi birnin, a lokacin da mutanen suka taso mana yadda suka yi dā, sai mu guje musu.
6 until, pursuing us, they are drawn away from the city. For they will think that we are fleeing as before.
Za su bi mu har su yi nisa da birnin, gama za su ce, ‘Suna gudu kamar yadda suka yi dā.’ Saboda haka lokacin da muka guje musu,
7 Then, while we are fleeing and they are pursuing, you shall rise up from the ambush, and you shall lay waste to the city. And the Lord your God will deliver it into your hands.
sai ku tashi daga inda kuka yi kwanto, ku ci birnin da yaƙi, Ubangiji Allahnku zai ba da shi a hannunku.
8 And when you have seized it, set it on fire. And you shall do all that I have ordered.”
Lokacin da kuka ƙwace birnin, sai ku sa masa wuta. Ku yi abin da Ubangiji ya umarta. Ku tabbata kun yi abubuwan da na ce.”
9 And he sent them away, and they traveled to the place of the ambush, and they settled between Bethel and Ai, toward the western region of the city of Ai. But Joshua remained for that night in the midst of the people.
Sai Yoshuwa ya sallame su, suka kuma tafi wurin da za su yi kwanto, suka kwanta suna fako tsakanin Betel da Ai, yamma da Ai, amma Yoshuwa ya kwana tare da mutanen.
10 And rising at first light, he reviewed his troops, and he went up, with the elders at the front of the army, surrounded by an auxiliary of fighters.
Kashegari da sassafe Yoshuwa ya tattara mutanensa, sai shi da shugabannin Isra’ilawa suka sha gaba suka taka zuwa Ai.
11 And when they had arrived, and had ascended from the opposite side of the city, they stood toward the northern region of the city. And there was a valley in the middle, between them and the city.
Dukan sojojin da suke tare da shi suka nufi birnin, da suka kai kuwa sai suka kafa sansaninsu a arewancin Ai. Tsakaninsu da Ai akwai kwari.
12 Now he had chosen five thousand men, and he had positioned them in ambush between Bethel and Ai, at the western part of the same city.
Yoshuwa ya sa mutum dubu biyar suka yi kwanto tsakanin Betel da Ai, a yammancin birnin.
13 Yet truly, all the remainder of the army was arranged in a line to the north, so that the very end of that multitude reached to the western region of the city. Then Joshua went out that night, and he stood in the middle of the valley.
Mutanen suka kafa sansaninsu arewa da birnin, sansani na’yan kwanto kuwa yana yamma da birnin, amma Yoshuwa ya kwana a kwarin.
14 And when the king of Ai had seen this, he hurried in the morning, and he went out with the entire army of the city. And he arranged them in a line opposite the desert, not knowing that an ambush lay hidden behind his back.
Sa’ad da sarkin Ai ya ga haka, shi da duk mutanen birnin suka hanzarta da sassafe don su gamu da Isra’ilawa, su yi yaƙi da su a wani wurin da yake fuskantar Araba. Amma bai san cewa an yi masa kwanto a bayan birnin ba.
15 Yet truly, Joshua, and all of Israel, withdrew from the place, pretending to be afraid, and fleeing along the way of the wilderness.
Yoshuwa da duk Isra’ilawa suka bari aka fafare su, sai suka gudu zuwa cikin jeji.
16 And they pursued them, shouting together and encouraging one another. And when they had withdrawn from the city,
Aka kira duk mazan Ai su fafare su, suka kuwa fafari Yoshuwa, aka yaudare su suka yi nisa da birnin.
17 and indeed not one remained in the city of Ai and of Bethel who did not pursue after Israel, (leaving the towns open after they had rushed out, )
Ba namijin da ya rage a Ai ko Betel da bai fita don yă fafari Isra’ilawa ba. Suka bar birnin a buɗe, suka tafi fafarar Isra’ilawa.
18 the Lord said to Joshua: “Lift up the shield that is in your hand, toward the city of Ai. For I will deliver it to you.”
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka riƙe māshin da yake hannunka ka nuna wajen Ai, gama zan ba da birnin a hannunka.” Yoshuwa kuwa ya miƙa māshin ta wajen Ai.
19 And when he had lifted up the shield toward the city, the ambush, which lay hidden, rose up quickly. And advancing to the city, they seized it, and set it on fire.
Da yin haka kuwa sai mutanen da suka yi kwanto suka tashi nan da nan daga inda suke, suka nufi birnin a guje, suka shiga suka ci birnin da yaƙi, suka kuma cinna mata wuta da sauri.
20 Now the men of the city who were pursuing Joshua, looking back and seeing the smoke of the city rising up even to heaven, were no longer able to flee in one direction or another, especially since those who had pretended to flee, and who were heading toward the wilderness, had turned back very strongly against those who were pursuing them.
Mutanen Ai suka juya suka ga hayaƙin birninsu yana tashi sama, amma ba yadda za su iya tsira ta ko’ina, gama Isra’ilawan da suke gudu zuwa cikin jeji suka juya suka fara fafarar waɗanda suke fafararsu.
21 And Joshua, and all of Israel, seeing that the city had been captured, and that the smoke of the city was ascending, returned and struck down the men of Ai.
Lokacin da Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ga waɗanda suka yi kwanto sun ci birnin da yaƙi, hayaƙi kuwa ya cika birnin, sai suka juya suka kai wa mutanen Ai hari.
22 Then too, those who had seized and set the city on fire, departing from the city toward their own men, began to strike the enemies in the middle. Therefore, since the adversaries were cut off from both sides, none of so great a multitude was saved.
Mutanen da suka yi kwanto su ma suka fito daga birnin suka tasar musu, ya zama an kama su a tsakiya, ga Isra’ilawa daga kowane gefe. Isra’ilawa kuwa suka karkashe su duka ba su bar wani da rai ba, ba kuma wanda ya tsere.
23 Also, they apprehended the king of the city of Ai, alive, and they brought him before Joshua.
Amma suka tafi da sarkin Ai da rai suka kawo shi wurin Yoshuwa.
24 And so, after all were slain who had pursued Israel fleeing toward the wilderness, and after they fell by the sword in the same place, the sons of Israel returned and struck the city.
Da Isra’ilawa suka gama kashe duk mutanen Ai a filaye da kuma a cikin jeji inda suka fafare su, kuma da aka karkashe kowane mutumin Ai da takobi sai dukan Isra’ilawa suka koma Ai suka karkashe duk waɗanda suke cikinsa.
25 Now there were twelve thousand persons who had fallen on the same day, from man even to woman, the entire city of Ai.
A ranan nan, dukan mutanen Ai da aka kashe, mutum dubu goma sha biyu ne maza da mata.
26 Truly Joshua did not draw back his hand, which he had stretched out on high, keeping hold of the shield until all the inhabitants of Ai were put to death.
Gama Yoshuwa bai janye hannunsa da yake riƙe da māshinsa ba har sai da ya hallaka dukan mazaunan Ai.
27 Then the sons of Israel divided among themselves the cattle and the plunder of the city, just as the Lord had instructed Joshua.
Amma Isra’ilawa suka kwashe ganima da dabbobin birnin nan yadda Ubangiji ya umarci Yoshuwa.
28 And he set fire to the city, and he caused it to be a perpetual tomb.
Yoshuwa kuwa ya ƙone Ai, ya mai da ita tarin ƙasa, ta zama kufai har wa yau.
29 Also, he suspended the king on a gallows, until evening and the setting of the sun. And Joshua instructed, and they took down his dead body from the hanging tree. And they cast it at the very entrance of the city, gathering a great pile of stones upon it, which remains even to the present day.
Ya rataye sarkin Ai a kan itace, ya bar shi a can har yamma. Da rana ta fāɗi, Yoshuwa ya umarta a ɗauke gawar sarkin a jefa a gaban ƙofar birnin. Suka kuma tara manyan duwatsu a kan gawar, tsibin na nan har wa yau.
30 Then Joshua built an altar to the Lord, the God of Israel, on Mount Ebal,
Yoshuwa kuwa ya yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila bagade a Dutsen Ebal,
31 just as Moses, the servant of the Lord, had instructed to the sons of Israel, and this was written in the book of the law of Moses: truly, an altar of uncut stones, which iron has not touched. And he offered holocausts upon it to the Lord, and he immolated victims as peace-offerings.
kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarci Isra’ilawa. Ya gina bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Littafin Dokoki na Musa, bagade na duwatsun da ba a sassaƙa su ba, waɗanda ba wani ƙarfen da ya taɓa su. Suka miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kai.
32 And he wrote on the stones, the Deuteronomy of the law of Moses, which he had set in order before the sons of Israel.
A can, a gaban Isra’ilawa, Yoshuwa ya rubuta dokokin Musa a kan duwatsun.
33 Then all the people, and those greater by birth, and the commanders and judges were standing on both sides of the ark, in the sight of the priests who were carrying the ark of the covenant of the Lord, with both the new arrival and the native born, one half part of them beside Mount Gerizim, and one half beside Mount Ebal, just as Moses, the servant of the Lord, had instructed. And first, certainly, he blessed the people of Israel.
Sai Isra’ilawa duka, da baƙi, da haifaffun gida, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, suka tsaya a gefe-gefen akwatin alkawarin Ubangiji, suna fuskantar waɗanda suke ɗauke da shi, wato, firistoci waɗanda su ne Lawiyawa. Rabin mutanen suka tsaya a gaban Dutsen Gerizim, rabinsu kuma suka tsaya a gaban Dutsen Ebal, kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya riga ya umarta, cewa su sa wa mutanen Isra’ilawa albarka.
34 After this, he read all the words of the blessing and the cursing, and all the things that were written in the book of the law.
Bayan haka, Yoshuwa ya karanta duk abin da yake a cikin Dokoki, albarku da la’anoni, kamar yadda suke a rubuce a cikin Littafin Dokoki.
35 He left nothing untouched out of those things that Moses had ordered, and he repeated everything before the entire multitude of Israel, with the women and the little ones, and the new arrivals who were staying among them.
Babu wata kalmar da Musa ya umarta da Yoshuwa bai karanta wa dukan taron Isra’ilawa ba, haɗe da mata, da yara, da baƙin da suke zama tare da su.

< Joshua 8 >