< Joshua 9 >

1 And when these things were heard, all the kings across the Jordan, who lived among the mountains and plains, along the coastline and shores of the great sea, also those who were living near Lebanon, the Hittite, and the Amorite, the Canaanite, the Perizzite, and the Hivite, and the Jebusite,
To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
2 gathered themselves together, so that they might fight against Joshua and Israel, with one mind and with the same resolve.
suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
3 But those who were living in Gibeon, hearing all that Joshua had done to Jericho and Ai,
Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
4 planning cleverly, took for themselves provisions, placing old sacks upon their donkeys, and wineskins that had torn and been sewed up,
sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
5 and having very old shoes, which had been sewn with patches indicating their age, and being clothed in old garments, having also loaves, which they carried as food for the journey, which were hard and broken into pieces.
Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
6 And they traveled to Joshua, who at that time was staying in the camp at Gilgal. And they said to him, and to all of Israel with him, “We have come from a far away land, desiring to make peace with you.” And the sons of Israel responded to them, and said,
Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
7 “Perhaps instead, you live in the land which ought to be ours by lot, and we would be unable to form a pact with you.”
Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
8 But they said to Joshua, “We are your servants.” And Joshua said to them: “But who are you? And where are you from?”
Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
9 They responded: “Your servants have arrived, from a very far away land, in the name of the Lord, your God. For we have heard about the fame of his power, all the things that he has done in Egypt,
Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
10 and to the two kings of the Amorites, who were beyond the Jordan: Sihon, the king of Heshbon, and Og, the king of Bashan, who was at Ashtaroth.
da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
11 And our elders, and all the inhabitants of our land, have said to us: ‘Take in hand provisions for the very long journey, and meet with them, and say: We are your servants; form a pact with us.’
Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
12 Lo, the loaves were taken up warm when we departed from our houses, so that we might come to you. Now they have become dry and broken, due to age.
Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
13 These wineskins were new when we filled them, now they are torn and broken. The garments we are wearing, and the shoes we have on our feet, due to the great length of the distance, have become worn and are nearly consumed.”
Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
14 And so they accepted this, because of their provisions, and they did not consult the mouth of the Lord.
Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
15 And Joshua made peace with them, and entering into a pact, he promised that they would not be put to death. The leaders of the multitude also swore to them.
Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
16 Then, three days after the pact was formed, they heard that they lived in the vicinity, and that they would soon be among them.
Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
17 And so the sons of Israel moved the camp, and they arrived at their cities on the third day, those which are called: Gibeon, and Chephirah, and Beeroth, and Kiriath-jearim.
Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
18 And they did not strike them, because the leaders of the multitude had sworn to them in the name of the Lord, the God of Israel. And so all of the common people murmured against the leaders.
Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
19 And they responded to them: “We have sworn to them in the name of the Lord, the God of Israel, and for that reason, we are not able to touch them.
Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
20 But we shall do this to them: Certainly, let them be preserved so that they may live, lest the wrath of the Lord be stirred up against us, since we would have sworn falsely.
Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
21 But though they live, let them serve the entire multitude by cutting wood and carrying water.” And while they were discussing these things,
Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
22 Joshua called the Gibeonites, and he said to them: “Why would you be willing to deceive us by fraud, saying, ‘We live very far away from you,’ when you are in our midst?
Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
23 Therefore, you shall be under a curse, and your stock shall not cease to be cutters of wood and carriers of water, into the house of my God.”
Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
24 And they responded: “It was reported to us, your servants, that the Lord your God had promised his servant Moses that he would give you the entire land, and that he would destroy all its inhabitants. Therefore, we were very afraid, and we made a provision for our lives, compelled by the dread of you, and we undertook this counsel.
Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
25 And now we are in your hand. Act toward us as it seems good and right to you.”
Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
26 Therefore, Joshua did just as he had said, and he freed them from the hand of the sons of Israel, so that they would not be killed.
Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
27 And he decreed on that day, that they would be in the ministry of all the people and of the altar of the Lord, cutting wood and carrying water, even until this present time, in the place which the Lord had chosen.
A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.

< Joshua 9 >