< Joshua 3 >

1 And so, Joshua arose in the night, and he moved the camp. And they departed from Shittim, and they went to the Jordan: he, and all the sons of Israel, and they remained there for three days.
Kashegari Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Shittim suka nufi Urdun inda suka sauka kafin su haye.
2 After these things unfolded, announcers passed through the midst of the camp,
Bayan kwana uku sai shugabannin suka zazzaga sansani, suna
3 and they began to proclaim: “When you will see the ark of the covenant of the Lord your God, and the priests of the stock of Levi carrying it, you also shall rise up and follow those who are going before you.
ba da umarni ga mutane, suna cewa, “Lokacin da kuka ga akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku, da firistoci waɗanda su ne Lawiyawa, suna ɗauke da shi, sai ku tashi daga inda kuke, ku bi shi.
4 And let there be, between you and the ark, the space of two thousand cubits, so that you may be able to see it from far away, and to know along which way you should advance. For you have not walked this way before. And be careful that you do not approach the ark.”
A ta haka za ku san inda za ku bi, gama ba ku taɓa bin hanyar ba. Sai dai ku ɗan ba da rata wajen yadi ɗari tara tsakaninku da akwatin alkawari, kada ku kusace shi.”
5 And Joshua said to the people: “Be sanctified. For tomorrow the Lord will accomplish miracles among you.”
Yoshuwa ya ce wa mutane, “Ku tsarkake kanku, gama gobe Ubangiji zai yi abubuwan al’ajabi a cikinku.”
6 And he said to the priests: “Take up the ark of the covenant, and go before the people.” And they fulfilled the orders, and they took it and walked before them.
Yoshuwa ya ce wa firistoci, “Ku ɗauki akwatin alkawari ku sha gaba.” Sai suka ɗauki akwatin alkawari suka wuce gaban sauran jama’a.
7 And the Lord said to Joshua: “Today I will begin to exalt you in the sight of all Israel, so that they may know that, just as I was with Moses, so also am I with you.
Ubangiji kuwa ya ce wa Yoshuwa, “Yau, zan fara ɗaukaka ka a gaban Isra’ilawa duka don su sani cewa ina tare da kai kamar yadda na kasance tare da Musa.
8 Now instruct the priests, who are carrying the ark of the covenant, and say to them, ‘When you will have entered into a part of the water of the Jordan, stand still in it.’”
Ka ce wa firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawari, ‘Sa’ad da kuka kai bakin Urdun, ku shiga cikin ruwan ku tsaya.’”
9 And Joshua said to the sons of Israel, “Approach to here, and listen to the word of the Lord your God.”
Yoshuwa ya ce wa Isra’ilawa, “Ku zo nan ku ji maganar Ubangiji Allahnku.
10 And again, he said: “By this shall you know that the Lord, the living God, is in your midst, and that he shall scatter in your sight, the Canaanite and the Hittite, the Hivite and the Perizzite, likewise the Girgashite, and the Jebusite, and the Amorite.
Ta haka ne za ku san cewa Allah mai rai yana tare da ku, kuma ba shakka a gabanku za ku gani zai kore Kan’aniyawa, Hittiyawa, Hiwiyawa, Ferizziyawa, Girgashiyawa, Amoriyawa da Yebusiyawa.
11 Behold, the ark of the covenant of the Lord of all the earth shall go before you through the Jordan.
Ku duba, akwatin alkawarin Ubangiji na dukan duniya zai yi gaba cikin Urdun kafin ku.
12 Prepare twelve men from the tribes of Israel, one from each tribe.
Yanzu sai ku zaɓi mutum goma sha biyu daga kabilan Isra’ila, ɗaya daga kowace kabila.
13 And when the priests who are carrying the ark of the Lord, the God of the entire earth, will have placed the steps of their feet in the waters of the Jordan, the waters that are lower will run down and pass away, and those that are approaching above will stand together in a mass.”
Kuma da firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji, Ubangiji dukan duniya, sun sa ƙafa cikin ruwan kogin Urdun, ruwan da yake gudu a rafin zai tsaya cik yă taru a wuri ɗaya.”
14 And the people departed from their tents, so that they might cross the Jordan. And the priests who were carrying the ark of the covenant were advancing before them.
Saboda haka sa’ad da mutanen suka tashi don su ƙetare Urdun, firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawarin suka sha gaba.
15 And as soon as they entered into the Jordan, and their feet were dipped in a portion of the water, (now the Jordan, since it was the time of the harvest, had filled the banks of its channel, )
Da kaka Urdun yakan cika makil da ruwa. Duk da haka da zarar firistoci masu ɗauke da akwatin alkawari suka tsoma ƙafafunsu a gefen ruwa,
16 the descending waters stood still in one place, and, swelling up like a mountain, they were seen from far away, from the city that is called Adam, even as far as the place of Zarethan. But those that were lower ran down into the Sea of the Wilderness, (which is now called the Dead Sea, ) until they entirely passed away.
sai ruwan da yake gangarowa ya tsaya, ya tattaru a wuri ɗaya ya yi tudu daga nan har zuwa wani garin da ake kira Adam kusa da Zaretan, ruwan da yake gangarowa zuwa Tekun Araba (Tekun Gishiri) kuma ya yanke gaba ɗaya. Sai mutane suka ƙetare kusa da Yeriko.
17 Then the people advanced opposite Jericho. And the priests who were carrying the ark of the covenant of the Lord were standing, fully-dressed, upon dry soil in the midst of the Jordan, and all the people passed over, through the channel that was dried up.
Firistocin kuwa da suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya daram a kan busasshiyar ƙasa a tsakiyar Urdun a lokacin da Isra’ilawa suka ƙetarewa, har sai da dukan mutane suka gama ƙetarewa.

< Joshua 3 >