< Joshua 10 >

1 When Adonizedek, the king of Jerusalem, had heard these things, specifically, that Joshua had seized Ai, and had overthrown it, (for just as he had done to Jericho and its king, so did he do to Ai and its king, ) and that the Gibeonites had fled over to Israel, and were now their confederates,
Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya ji cewa Yoshuwa ya ci Ai da yaƙi ya kuma hallaka ta sarai, ya yi wa Ai da sarkinta abin da ya yi wa Yeriko da sarkinta, mutanen Gibeyon kuwa sun yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, suna kuma zama kusa da su.
2 he was very afraid. For Gibeon was a great city, and was one of the royal cities, and was greater than the town of Ai, and all its warriors were very strong.
Shi da mutanensa suka ji tsoron wannan sosai, gama Gibeyon muhimmiyar birni ce, har ma kamar ɗaya daga cikin biranen sarauta, ya ma fi Ai girma, mazanta duka kuwa mayaƙa ne na ƙwarai.
3 Therefore, Adonizedek, the king of Jerusalem, sent to Hoham, the king of Hebron, and to Piram, the king of Jarmuth, and also to Japhia, the king of Lachish, and to Debir, the king of Eglon, saying:
Saboda haka sai Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya roƙi Hoham sarkin Hebron, Firam sarkin Yarmut, Yafiya sarkin Lakish da Debir sarki Eglon ya ce,
4 “Ascend to me, and bring troops, so that we may fight against Gibeon. For it has fled over to Joshua and the sons of Israel.”
“Ku zo ku taimake ni in kai wa Gibeyon hari. Domin sun yi yarjejjeniya ta salama da Yoshuwa da Isra’ilawa.”
5 And so, having assembled, the five kings of the Amorites, the king of Jerusalem, the king of Hebron, the king of Jarmuth, the king of Lachish, the king of Eglon, together with their armies, went up and encamped around Gibeon, laying siege to it.
Sai sarakunan nan biyar na Amoriyawa, sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon suka haɗa sojojinsu. Suka je dukansu suka yi shirin kai wa Gibeyon hari.
6 But the inhabitants of the city of Gibeon, when it was besieged, sent to Joshua, who was then staying in the camp at Gilgal. And they said to him: “May you not draw back your hands from helping your servants. Come quickly, and free us, and bring troops. For all the kings of the Amorites, who live in the mountains, have gathered together against us.”
Sai mutanen Gibeyon suka aika zuwa wurin Yoshuwa a sansani a Gilgal, “Kada ka juya wa bayinka baya, ka zo da sauri ka cece mu! Ka taimake mu domin sarakunan Amoriyawa duka daga kan tudu sun haɗa ƙarfinsu tare za su tasar mana.”
7 And Joshua ascended from Gilgal, and the entire army of warriors with him, very strong men.
Saboda haka Yoshuwa ya tashi da rundunarsa duka, tare da dukan jarumawansa.
8 And the Lord said to Joshua: “You should not fear them. For I have delivered them into your hands. None of them will be able to withstand you.”
Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu; na ba ka su a hannunka. Ba waninsu da zai iya tsayayya da kai.”
9 And so Joshua, ascending from Gilgal throughout the night, rushed upon them suddenly.
Bayan sun yi tafiya dukan dare daga Gilgal, Yoshuwa ya auko musu ba labari.
10 And the Lord set them in disarray before the face of Israel. And he crushed them in a great defeat at Gibeon, and he pursued them along the way of the ascent to Beth-horon, and he struck them down, even as far as Azekah and Makkedah.
Ubangiji ya sa suka ruɗe a gaban Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka yi babbar nasara a kansu a Gibeyon. Isra’ilawa suka fafare su a kan hanyar zuwa Bet-Horon suka karkashe su duka har zuwa Azeka da Makkeda.
11 And while they were fleeing from the sons of Israel, and were on the descent of Beth-horon, the Lord cast great stones from heaven upon them, as far as Azekah. And many more were killed by the hailstones, than were struck down by the swords of the sons of Israel.
Suna guje wa Isra’ilawa suna gangarawa a kan hanyar Bet-Horon har zuwa Azeka, sai Ubangiji ya turo manyan duwatsu daga sararin sama suka karkashe su, waɗanda manyan duwatsun suka kashe sun fi waɗanda Isra’ilawa suka kashe da takobi.
12 Then Joshua spoke to the Lord, on the day that he handed over the Amorite in the sight of the sons of Israel, and he said before them: “O sun, you shall not move toward Gibeon! O moon, you shall not move toward the valley of Aijalon!”
A ranar da Ubangiji ya ba da Amoriyawa a hannun Isra’ilawa, Yoshuwa ya ce wa Ubangiji a gaban Isra’ilawa, “Ke rana, ki tsaya cik a Gibeyon Kai wata, ka je Kwarin Aiyalon.”
13 And the sun and the moon stood still, until the people had avenged themselves of their enemies. Has this not been written in the book of the just? And so the sun stood still in the midst of heaven, and it did not hurry to its rest for the space of one day.
Sai rana ta tsaya cik, wata kuma ya tsaya, har sai da al’ummar ta ɗauki fansa a kan abokan gābanta, kamar yadda aka rubuta a cikin littafin Yashar. Rana ta tsaya a sararin sama, ba tă fāɗi ba har kusan yini guda.
14 Never before and never after was there so long a day, as when the Lord obeyed the voice of a man, and fought for Israel.
Ba a taɓa ganin abu haka ba ko dā can, ranar da Ubangiji ya saurari mutum. Ba shakka Ubangiji yana yaƙi domin Isra’ilawa.
15 And Joshua returned, with all of Israel, into the camp of Gilgal.
Sai Yoshuwa ya koma sansanin Gilgal tare da dukan Isra’ilawa.
16 For the five kings had fled, and had hidden themselves in a cave, near the city of Makkedah.
Sarakunan guda biyar suka gudu, suka ɓuya a cikin kogo a Makkeda.
17 And it was reported to Joshua that the five kings had been found hidden in a cave, near the city of Makkedah.
Lokacin da aka gaya wa Yoshuwa cewa an sami sarakunan nan biyar a ɓoye a cikin kogo a Makkeda.
18 And he instructed his companions and said: “Roll vast stones to the mouth of the cave, and station attentive men who will keep them closed.
Sai ya ce, “Ku mirgina manyan duwatsu ku rufe bakin kogon, sai ku sa waɗannan mutane su yi tsaron kogon.
19 But as for you, do not stay here; instead, pursue the enemies, and cut down the lattermost of those who are fleeing. You shall not permit those whom the Lord God has delivered into your hands to enter into the protection of their cities.”
Amma kada ku tsaya a can! Ku fafari abokan gābanku, ku kai musu hari ta baya, kada ku bari su kai biranensu, gama Ubangiji Allahnku ya ba da su a hannunku.”
20 Thus, the adversaries were struck down in a great defeat, and having been nearly consumed, even to utter annihilation, those who were able to escape from Israel entered into fortified cities.
Saboda haka Yoshuwa da Isra’ilawa suka hallaka su da yawa ƙwarai, amma’yan kaɗan ɗin da suka rage suka tsere zuwa cikin biranensu masu kāriya.
21 And the entire army returned to Joshua at Makkedah, where they were then encamped, in good health and in their full numbers. And no one dared to move his tongue against the sons of Israel.
Dukan rundunar kuma suka dawo sansanin Makkeda tare da Yoshuwa, ba abin da ya same su. Ba wanda ya sāke tsokanar Isra’ilawa.
22 And Joshua instructed, saying, “Open the mouth of the cave, and bring forward to me the five kings, who are hidden within it.”
Yoshuwa ya ce, “Ku buɗe bakin kogon ku kawo mini sarakunan nan guda biyar.”
23 And the ministers did just as they had been ordered. And they led out to him the five kings from the cave: the king of Jerusalem, the king of Hebron, the king of Jarmuth, the king of Lachish, the king of Eglon.
Sai suka kawo sarakunan biyar daga cikin kogo; sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon.
24 And when they had been led out to him, he called all the men of Israel, and he said to the leaders of the army who were with him, “Go, and place your feet upon the necks of these kings.” And when they had gone and had tread their feet upon the necks of those who were thrown down,
Sa’ad da aka kawo sarakunan nan wurin Yoshuwa, ya kira dukan Isra’ilawa ya ce wa shugabannin rundunoni waɗanda suke tare da shi, “Ku zo nan ku taka wuyan sarakunan nan.” Sai suka zo suka taka wuyansu.
25 he spoke to them again: “Do not be afraid, and do not dread. Be strengthened and be steadfast. For so will the Lord do to all your enemies, against whom you fight.”
Yoshuwa ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ko kuwa ku razana, amma ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Haka Ubangiji zai yi da duk abokan gāban da za ku yi yaƙi da su.”
26 And Joshua struck them down and killed them, and he suspended them on five gallows. And they hung there until evening.
Sai Yoshuwa ya karkashe waɗannan sarakuna guda biyar, ya kuma rataye kowannensu a bisa itace inda jikunansu suka kasance har yamma.
27 And when the sun had set, he instructed his assistants that they should take them down from the gallows. And having been taken down, they cast them into the cave, where they had lain hidden, and they set vast stones at its mouth, which remain, even to the present.
Da yamma Yoshuwa ya ba da umarni a sauko da su daga itatuwan a jefa su cikin kogon da suka ɓuya. Aka sa manyan duwatsu aka rufe bakin kogon, suna a can har wa yau.
28 Also on the same day, Joshua seized Makkedah, and he struck it with the edge of the sword, and he put to death its king and all its inhabitants. He did not leave in it even the smallest remains. And he did to the king of Makkedah, just as he had done to the king of Jericho.
A ranan nan Yoshuwa ya ci Makkeda da yaƙi. Ya karkashe mutanen tare da sarkinta. Bai bar wani da rai ba. Ya yi wa sarkin Makkeda yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
29 Then he went on, with all of Israel, from Makkedah to Libnah, and he fought against it.
Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Makkeda zuwa Libna, suka kai mata hari.
30 And the Lord delivered it, with its king, into the hands of Israel. And they struck the city with the edge of the sword, and all its inhabitants. They did not leave in it any remains. And they did to the king of Libnah, just as they had done to the king of Jericho.
Ubangiji kuma ya ba da ƙasar da sarkinta a hannun Yoshuwa. Yoshuwa ya karkashe kowa ya hallaka birnin, bai bar wani da rai ba. Ya kuma yi wa sarkin yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
31 From Libnah, with all of Israel, he went on to Lachish. And taking positions around it with his army, he besieged it.
Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Libna zuwa Lakish; suka yi shiri suka kai mata hari.
32 And the Lord delivered Lachish into the hands of Israel, and he seized it on the following day, and he struck it with the edge of the sword, and every soul that was in it, just as he had done to Libnah.
Ubangiji ya ba da Lakish a hannun Isra’ilawa, a rana ta biyu kuwa Yoshuwa ya ci nasara a kansu. Ya karkashe duk mutanen birnin ya kuma hallaka birnin, kamar yadda ya yi a Libna.
33 At that time, Horam, the king of Gezer, went up so that he might assist Lachish. And Joshua struck him with all his people, even unto utter annihilation.
Horam sarkin Gezer kuwa ya zo don yă taimaki Lakish, amma Yoshuwa ya haɗa duk da shi da rundunarsa ya ci su da yaƙi, har bai bar waninsu da rai ba.
34 And he went on from Lachish to Eglon, and he surrounded it.
Yoshuwa kuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Lakish zuwa Eglon; suka yi shiri suka kai mata hari.
35 And he also defeated it on the same day. And he struck all the souls that were in it with the edge of the sword, in accord with all that he had done to Lachish.
A ranan nan suka ci ƙasar da yaƙi, suka buge ta, suka karkashe kowa da takobi kamar dai yadda suka yi a Lakish.
36 He also ascended, with all of Israel, from Eglon into Hebron, and he fought against it.
Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Eglon zuwa Hebron suka kai hari a can.
37 He seized it and struck it with the edge of the sword, likewise with its king, and all the towns of that region, and all the souls that were staying in it. He did not leave any remains in it. Just as he had done to Eglon, so also did he do to Hebron, consuming with the sword all that he found within it.
Suka ci birnin da yaƙi, suka karkashe mazaunanta, da sarkin, har da ƙauyukan, ba wanda ya tsira kamar yadda ya yi wa Eglon. Ya hallakar da ita sarai duk da kowane mutum da yake cikinta.
38 Returning from there to Debir,
Yoshuwa da Isra’ilawa duka suka juya suka kai wa Debir hari,
39 he seized it and laid waste to it, likewise with its king. And all the surrounding towns, he struck with the edge of the sword. He did not leave in it any remains. Just as he had done to Hebron and Libnah, and to their kings, so did he do to Debir and to its king.
suka hallaka birnin, da sarkinta da ƙauyukanta, suka karkashe dukan mazaunan wurin, ba su bar wani da rai ba. Suka yi wa Debir da sarkinta yadda suka yi wa Libna da sarkinta da kuma Hebron.
40 And so Joshua struck the entire land, the mountains, and the south, and the plains, and the descending slopes, with their kings. He did not leave in it any remains, but he put to death all that was able to breathe, just as the Lord, the God of Israel, had instructed him,
Yoshuwa ya cinye yankin duka da yaƙi, haɗe da na kan tudu, da Negeb, da kwarin yamma, da filayen cikin duwatsu tare da sarakunansu duka. Bai bar wani da rai ba, ya kashe duk wani mai numfashi, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ilawa ya umarta.
41 from Kadesh-barnea, as far as Gaza, with all the land of Goshen, as far as Gibeon.
Yoshuwa ya ci su da yaƙi daga Kadesh Barneya zuwa Gaza, da kuma daga dukan yankin Goshen zuwa Gibeyon.
42 And all their kings and their regions, he seized and destroyed with a single attack. For the Lord, the God of Israel, fought on his behalf.
Yoshuwa kuwa ya cinye sarakunan nan duka da ƙasashensu gaba ɗaya gama Ubangiji, Allah na Isra’ila ne ya yi yaƙi domin Isra’ilawa.
43 And he returned, with all of Israel, to the place of the encampment at Gilgal.
Yoshuwa kuwa ya dawo da dukan Isra’ilawa zuwa sansani a Gilgal.

< Joshua 10 >