< Job 8 >

1 But Baldad the Suhite, responding, said:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 How long will you speak this way, so that the words of your mouth are like a changeable wind?
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3 Does God supplant judgment, or does the Almighty subvert that which is just?
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4 And if now your children have sinned against him, and he has dismissed them into the power of their iniquity,
Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5 even so, you should arise early to God, so as to beseech the Almighty.
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6 If you approach with purity and honesty, he will quickly be attentive to you, and a peaceful life will repay your righteousness,
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7 so much so that, if your former things were small, your latter things would be multiplied greatly.
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
8 For inquire of the earliest generation, and investigate diligently the history of the fathers,
“Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
9 (of course, we are but of yesterday and are ignorant that our days on earth are like a shadow, )
gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
10 and they will teach you; they will speak with you and will offer you the eloquence of their hearts.
Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
11 Can the marsh plant live without moisture? Or can sedges grow without water?
Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
12 When it is still in flower, and has not been pulled up by hand, it withers before all other plants.
Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
13 Just so are the ways of all who forget God, and the hope of the hypocrite will perish.
Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
14 His frenzy will not please him, and his faith will be like a spider’s web.
Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
15 He will lean on his house, and it will not stand; he will prop it up, but it will not rise.
Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
16 He seems to have moisture before the sun arrives; and at sunrise, his sprout shoots forth.
Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
17 His roots will crowd together over a heap of stones, and among the stones he will remain.
shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
18 If someone is devoured right beside him, he will deny him and will say: “I do not know you.”
Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
19 For this is the benefit of his way, that others in turn may spring up from the earth.
Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
20 God will not discard the simple, nor will he extend his hand to the spiteful,
“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
21 even until your mouth is filled with laughter and your lips with rejoicing.
Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
22 Those who hate you, will be clothed with confusion, and the tabernacle of the impious will not continue.
Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”

< Job 8 >