< Job 12 >

1 Then Job, answering, said:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Are you, therefore, alone among men, and will wisdom die with you?
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
3 And I have a heart just as you also do, and I am not inferior to you. For who is ignorant of these things, which you know?
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
4 He who is mocked by his friends as I am, will call upon God, and he will listen to him because it is the sincerity of the just that is being mocked.
“Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
5 The lamp that is despised in the thoughts of the rich is ready for the appointed time.
Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
6 The tabernacles of robbers are numerous, and they provoke God boldly; whereas, it is he who has given all things into their hands.
Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
7 In truth, ask the mules, and they will teach you, and the birds of the sky, and they will reveal to you.
“Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
8 Speak with the earth, and it will respond to you, and the fish of the sea will explain.
Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
9 Who is ignorant that the hand of the Lord has made all these things?
Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
10 In his hand is the soul of all the living and the spirit of all the flesh of mankind.
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
11 Does not the ear perceive words, and the palate, when eating, perceive flavor?
Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
12 In old age is wisdom, and in length of days is prudence.
Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
13 With him is wisdom and strength, he has counsel and understanding.
“Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
14 If he tears down, there is no one who can build up; if he encloses a man, there is no one who can open.
Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
15 If he restrains the waters, everything will dry up; and if he sends them forth, they will subdue the land.
Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
16 With him is strength and wisdom; he knows both the deceiver and he who is deceived.
Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
17 He leads advisors to a foolish end and judges to stupidity.
Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
18 He removes the belt of kings and encircles their waist with a rope.
Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
19 He leads away priests in dishonor and displaces nobles,
Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
20 altering the lips of those who speak the truth and sweeping away the teaching of the aged.
Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
21 He pours disdain upon the leaders, relieving those who had been oppressed.
Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
22 He reveals the depths of the darkness, and he brings the shadow of death into the light.
Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
23 He multiplies peoples, and destroys them, and, having been overthrown, he restores them anew.
yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
24 He transforms the heart of the leaders of the people on earth, and misleads those who in vain advance upon the inviolable.
Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
25 They will grope as in the darkness, not the light, and he will make them stagger like drunkards.
Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.

< Job 12 >