< Job 34 >

1 After proclaiming these things, Eliu now had this to say:
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 May the wise hear my words, and may the educated listen to me.
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 For the ear examines words, and the mouth discerns foods by the taste.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Let us choose judgment for ourselves, and let us consider among ourselves what is best.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 For Job has said: “I am just, yet God has subverted my judgment.
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 For, within my judgment, there is a lie: my vehement barbs are without any sin.”
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 What man is there that is like Job, who drinks up derision as if it were water,
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 who accompanies those who work iniquity, and who walks with impious men?
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 For he has said, “Man will not please God, even if he should travel with him.”
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 Therefore, prudent men, hear me: impiety is far from God, and iniquity is far from the Almighty.
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 For he will restore to man his works, and according to the ways of each, he will repay them.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 For truly, God will not condemn in vain, nor will the Almighty repudiate judgment.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 What other is established over the earth? Or whom has he placed over the world, which he made?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 But, if he directs his heart towards him, he will draw his spirit and breath to himself.
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 All flesh will fail together, and man will return to ashes.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 Therefore, if you have understanding, hear what is said, and heed the sound of my eloquence.
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Is he that does not love judgment able to be corrected? And how can you so greatly condemn him who is just?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 He says to the king, “You are an apostate.” He calls commanders impious.
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 He does not accept the reputation of leaders; nor does he recognize the tyrant as he contends against the poor. For all are the work of his hands.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 They will die suddenly, and the people will be troubled in the middle of the night, but they will pass through it, and the violent will be taken away without a hand.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 For his eyes are upon the ways of men, and he examines all of their steps.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 There is no darkness and no shadow of death, where those who work iniquity may be hidden.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 For it is no longer within the power of man to enter into judgment with God.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 He will break into many innumerable pieces, and he will cause others to stand up in their place.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 For he knows their works, and, as a result, he will bring the night, and they will be crushed.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 Just as the impious do, he has struck them in a place where they can be seen.
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 They, as if with great diligence, have withdrawn from him, and they refused to understand all his ways,
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 so that they caused the outcry of the needy to reach him, and he heard the voice of the poor.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 For, when he grants peace, who is there that can condemn? When he hides his face, who is there that can contemplate him, either among the nations, or among all men?
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 He causes a hypocritical man to reign because of the sins of the people.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 Therefore, since I have been speaking about God, I will not prevent you from doing the same.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 If I have erred, you may teach me; if I have spoken unfairly, I will add no more.
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Does God require this of you because it is displeasing to you? For you were the first to speak, and not I. But if you know something better, speak.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Let men of understanding speak to me, and let a wise man listen to me.
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 But Job has been speaking foolishly, and his words contain unsound teaching.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 My father, let Job be tested even to the end; may you not retreat from a man of iniquity.
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 For he adds blasphemy on top of his sins; nevertheless, let him be constrained to be among us, and then let him provoke God to judgment with his speeches.
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >