< Job 33 >

1 Therefore, hear my speeches, Job, and listen to all my words.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Behold, I have opened my mouth; let my tongue speak along with my throat.
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 My words are from my simple heart, and my lips will speak a pure judgment.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 The Spirit of God made me, and the breath of the Almighty gave me life.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 If you can, answer me, and oppose me to my face.
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Behold, God has made me, just as he also has made you, and I, likewise, have been formed of the same clay.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 So, truly, do not let my wonders terrify you, and do not let my eloquence be burdensome to you.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 For you have spoken in my hearing, and I have heard the voice of your words, saying:
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 “I am clean and without sin; I am immaculate, and there is no iniquity in me.
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 Yet he has discovered blame in me, and so he has treated me like his enemy.
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 He has put my feet in fetters; he has kept watch over all my ways.”
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 Therefore, it is for this reason that you have not been justified. For I tell you that God is greater than man.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 Do you contend against him because he has not responded to all of your words?
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 God speaks once, and he does not repeat the same thing a second time.
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 Through a dream in a vision of the night, when a deep sleep falls over men, and they are sleeping in their beds,
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 then, he opens the ears of men, and, educating them, he teaches discipline,
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 so that he may divert a man from the things that he is doing, and may free him from pride,
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 rescuing his soul from corruption and his life from passing away by the sword.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 Likewise, he rebukes by sorrow in bed, and he causes all of his bones to become weak.
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 Bread becomes abominable to him in his life, and, to his soul, the meat which before he desired.
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 His body will waste away, and his bones, which had been covered, will be revealed.
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 His soul has approached corruption, and his life has drawn near to what is deadly.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 If there were an angel speaking for him, one among thousands, to declare the fairness of the man,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 he will have mercy on him, and he will say, “Free him, so that he will not descend to destruction. I have found a reason to be favorable to him.
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 His body is consumed by suffering. Let him return to the days of his youth.”
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 He will beg pardon from God, and he will be soothing to him; and he will look upon his face in jubilation, and he will restore his justice to man.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 He will consider mankind, and he will say: “I have sinned and truly I have offended, yet I was not treated as I deserved.”
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 He has freed his soul from continuing into destruction, so that, in living, it may see the light.
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Behold, all these things God works three times within each one,
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 so that he may revive their souls from corruption and enlighten them with the light of life.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Pay attention Job, and listen to me; and remain silent, while I speak.
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 Yet, if you have anything to say, answer me and speak, for I want you to be treated justly.
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 But if you do not have anything to say, then listen to me. Be quiet and I will teach you wisdom.
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”

< Job 33 >