< Job 30 >

1 But now, those younger in years scorn me, whose fathers I would not have seen fit to place with the dogs of my flock,
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2 the strength of whose hands was nothing to me, and they were considered unworthy of life itself.
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3 They were barren from poverty and hunger; they gnawed in solitude, layered with misfortune and misery.
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4 And they chewed grass and the bark from trees, and the root of junipers was their food.
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5 They took these things from the steep valleys, and when they discovered one of these things, they rushed to the others with a cry.
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
6 They lived in the parched desert and in caves underground or above the rocks.
An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
7 They rejoiced among these kinds of things, and they considered it delightful to be under thorns.
Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
8 These are the sons of foolish and base men, not even paying any attention to the land.
Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
9 Now I become their song, and I have been made into their proverb.
“Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10 They loathe me, and so they flee far from me, and they are not reluctant to spit in my face.
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
11 For he has opened his quiver and has afflicted me, and he has placed a bridle in my mouth.
Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
12 Immediately, upon rising, my calamities rise up to the right. They have overturned my feet and have pressed me down along their way like waves.
A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
13 They have diverted my journeys; they have waited to ambush me, and they have prevailed, and there was no one who might bring help.
Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
14 They have rushed upon me, as when a wall is broken or a gate opened, and they have been pulled down into my miseries.
Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
15 I have been reduced to nothing. You have taken away my desire like a wind, and my health has passed by like a cloud.
Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
16 But now my soul withers within myself, and the days of affliction take hold of me.
“Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
17 At night, my bone is pierced with sorrows, and those who feed on me, do not sleep.
Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
18 By the sheer number of them my clothing is worn away, and they have closed in on me like the collar of my coat.
A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
19 I have been treated like dirt, and I have been turned into embers and ashes.
Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
20 I cry to you, and you do not heed me. I stand up, and you do not look back at me.
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21 You have changed me into hardness, and, with the hardness of your hand, you oppose me.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22 You have lifted me up, and, placing me as if on the wind, you have thrown me down powerfully.
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23 I know that you will hand me over to death, where a home has been established for all the living.
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
24 Truly, then, you do not extend your hand in order to consume them, and if they fall down, you will save them.
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
25 Once, I wept over him who was afflicted, and my soul had compassion on the poor.
Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
26 I expected good things, but evil things have come to me. I stood ready for light, yet darkness burst forth.
Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
27 My insides have seethed, without any rest, for the days of affliction have prevented it.
Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
28 I went forth mourning, without anger, and rising up, I cried out in confusion.
Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
29 I was the brother of snakes, and the companion of ostriches.
Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
30 My skin has become blackened over me, and my bones have dried up because of the heat.
Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
31 My harp has been turned into mourning, and my pipes have been turned into a voice of weeping.
Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.

< Job 30 >