< Job 22 >

1 Then Eliphaz the Themanite responded by saying:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 Can man be compared with God, even if he were perfect in knowledge?
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
3 What advantage is it to God, if you were just? Or what do you provide for him, if your way should be immaculate?
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
4 Will he reprove you and take you to judgment for being afraid,
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
5 and not because of your many evil deeds and your infinite unfairness?
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
6 For you have taken away the collateral of your brothers without cause, and stripped them naked of their clothing.
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
7 You have not given water to the weary; you have taken bread away from the hungry.
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
8 By the strength of your arm, you took possession of the land, and you retain it by being the strongest.
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
9 You have sent widows away empty, and you have crushed the shoulders of orphans.
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
10 Because of this, you are surrounded by traps, and unexpected fears will disturb you.
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
11 And did you think that you would not see darkness and that you were not to be overwhelmed by the onrush of overflowing waters?
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
12 Have you not considered that God is higher than the heavens and is lifted above the height of the stars?
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
13 And you say: “Well, what does God know?” and, “He judges, as if through a fog,”
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
14 and, “The clouds are his hiding-place,” and, “He does not examine us closely,” and, “He makes his rounds at the limits of the heavens.”
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
15 Do you not want to tend the path of the ages, which wicked men have spurned?
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16 These were taken away before their time, and a flood overthrew their foundation.
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17 They said to God, “Withdraw from us,” and they treated the Almighty as if he could do nothing,
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18 though he had filled their houses with good things. May their way of thinking be far from me.
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
19 The just will see and will rejoice, and the innocent will mock them.
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
20 Has not their haughtiness been cut down, and has not fire devoured the remnants of them?
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
21 So, repose yourself with him and be at peace, and, in this way, you will have the best fruits.
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
22 Accept the law from his mouth, and place his words in your heart.
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
23 If you will return to the Almighty, you will be rebuilt, and you will put sinfulness far from your tabernacle.
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
24 He will give you stone in place of dirt, and torrents of gold in place of stone.
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
25 And the Almighty will be against your enemies, and silver will be gathered together for you.
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
26 Then will you flock together in delight over the Almighty, and you will lift up your face to God.
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
27 You will plead with him, and he will listen to you, and you will pay your vows.
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
28 You will decide on something, and it will come to you, and the light will shine in your ways.
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
29 For he who had been humbled, will be in glory; and he who will lower his eyes, will be the one saved.
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
30 The innocent will be saved, and he will be saved with purity in his hands.
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”

< Job 22 >