< Job 10 >

1 My soul is weary of my life. I will release my words against myself. I will speak in the bitterness of my soul.
“Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
2 I will say to God: Do not be willing to condemn me. Reveal to me why you judge me this way.
Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
3 Does it seem good to you, if you find fault with me and oppress me, the work of your own hands, and assist the counsel of the impious?
Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
4 Do you have bodily eyes? Or, just as man sees, will you see?
Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
5 Are your days just like the days of man, and are your years as the times of humans,
Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
6 so that you would inquire about my iniquity and examine my sin?
da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
7 And you know that I have done nothing impious, yet there is no one who can deliver from your hand.
Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
8 Your hands have made me and formed me all around, and, in this way, do you suddenly throw me away?
“Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
9 Remember, I ask you, that you have fashioned me like clay, and you will reduce me to dust.
Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
10 Have you not extracted me like milk and curdled me like cheese?
Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
11 You have clothed me with skin and flesh. You have put me together with bones and nerves.
Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
12 You have assigned to me life and mercy, and your visitation has preserved my spirit.
Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
13 Though you may conceal this in your heart, yet I know that you remember everything.
“Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
14 If I have sinned, and you have spared me for an hour, why do you not endure me to be clean from my iniquity?
In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
15 And if I should be impious, woe to me, and if I should be just, I will not lift up my head, being drenched with affliction and misery.
Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
16 And because of pride, you will seize me like a lioness, and having returned, you torment me to an extraordinary degree.
In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
17 You renew your testimony against me, and you multiply your wrath against me, and these punishments make war within me.
Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
18 Why did you lead me out of the womb? If only I had been consumed, so that no eye would ever see me!
“Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
19 I should have been as if I had not been: transferred from the womb to the tomb.
Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
20 Will not my few days be completed soon? Release me, therefore, so that I may lament my sorrows a little,
’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
21 before I depart and return no more to a land that is dark and covered with the fog of death,
kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
22 a land of misery and darkness, where the shadow of death, and nothing else but everlasting horror, dwells.
zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”

< Job 10 >