< Jeremiah 8 >

1 “In that time, says the Lord, they will cast out the bones of the kings of Judah, and the bones of its leaders, and the bones of the priests, and the bones of the prophets, and the bones of those who were living in Jerusalem, from their graves.
“‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
2 And they will spread them out before the sun and the moon and the entire army of the heavens, which they have loved, and served, and followed, and which they have sought and adored. They will not be collected, and they will not be buried. They will be like manure upon the face of the earth.
Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
3 And they will greatly prefer death to life: all those who will have been left from this wicked kindred, in all the forsaken places to which I will cast them out, says the Lord of hosts.
Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
4 And you will say to them: Thus says the Lord: He who falls, will he not rise again? And he who has been turned away, will he not return?
“Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
5 Then why have this people in Jerusalem turned away with a contentious loathing? They have taken hold of what is false, and they are not willing to return.
To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
6 I paid close attention and I listened carefully. No one is speaking what is good. There is no one who does penance for his sin, saying: ‘What have I done?’ They have all turned to their own course, like a horse rushing with fury into battle.
Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
7 The hawk in the heavens has known her time. The turtledove, and the swallow, and the stork have kept the time of their arrival. But my people have not known the judgment of the Lord.
Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
8 How can you say: ‘We are wise, and the law of the Lord is with us?’ Truly, the lying pen of the scribes has wrought falsehood.
“‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
9 The wise men have been confounded; they were terrified and captured. For they cast aside the word of the Lord, and there is no wisdom in them.
Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
10 Because of this, I will give their wives to outsiders and their fields to others as an inheritance. For from the least, even to the greatest, they all pursue avarice; from the prophet, even to the priest, they all act with deceit.
Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
11 And they healed the destruction of the daughter of my people with disgrace, by saying: ‘Peace, peace,’ though there was no peace.
Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
12 They have been confounded because they committed abomination. Or rather, they have not been confounded with shame, for they do not know how to blush. For this reason, they will fall among the fallen. In the time of their visitation, they will fall, says the Lord.
Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
13 When gathering, I will gather them together, says the Lord. There are no grapes on the vine, and there are no figs on the fig tree. The leaves have fallen. And I have given them the things that have passed away.”
“‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
14 “Why are we sitting still? Assemble, and let us enter the fortified city, and let us remain silent there. For the Lord our God has brought us to silence, and he has given us the water of gall as a drink. For we have sinned against the Lord.
Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
15 We expected peace, but there was nothing good. We expected a time of health, and behold, dread.”
Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
16 “From Dan, the snorting of his horses was heard; the entire land was shaken by the voice of the neighing of his fighters. And they arrived and devoured the land and its plenitude, the city and its inhabitants.
Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
17 For behold, I will send among you serpents, king snakes, against which there is no charm, and they will bite you, says the Lord.
“Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
18 My sorrow is beyond sorrow; my heart mourns within me.
Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
19 Behold, the voice of the daughter of my people from a far away land. Is the Lord not with Zion, and is her king not within her? Then why have they provoked me to wrath by their graven images, and by their strange vanities?
Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
20 The harvest has passed by, the summer is at an end, and we have not been saved.
“Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
21 Over the destruction of the daughter of my people, I am contrite and saddened; astonishment has taken hold of me.
Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
22 Is there no balm in Gilead? Or is there no physician there? Then why has the wound of the daughter of my people not been closed?”
Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?

< Jeremiah 8 >