< Jeremiah 6 >

1 “O sons of Benjamin, be strengthened in the midst of Jerusalem, and sound the trumpet in Tekoa, and lift up a banner over the house of Haccherem. For an evil has been seen from the north, with great destruction.
“Ku gudu neman mafaka, mutanen Benyamin! Ku gudu daga Urushalima! Ku busa ƙaho a Tekowa! Ku ba da alama a Bet-Hakkerem! Gama masifa tana zuwa daga arewa, mummunar hallaka ce kuwa.
2 I have compared the daughter of Zion to a beautiful and delicate woman.
Zan hallaka Diyar Sihiyona, kyakkyawa da kuma mai laulayi.
3 The pastors will come to her with their flocks. They have pitched their tents against her all around. Each one will feed those who are under his hand.
Makiyaya da garkunansu za su taso mata; za su kafa tentunansu kewaye da ita, kowanne yana lura da sashensa.”
4 ‘Sanctify a war against her! Rise up together, and let us ascend at midday.’ ‘Woe to us! For the day has declined; for the shadows of the evening have grown longer.’
“Mu shirya don yaƙi da ita! Ku tashi, bari mu fāɗa mata da tsakar rana! Amma, kaito, rana tana fāɗuwa, inuwar yamma kuwa sai ƙaran tsawo take.
5 ‘Rise up, and let us ascend in the night, and let us destroy her houses.’”
Saboda haka ku tashi, bari mu fāɗa mata da dare mu rurrushe kagaranta!”
6 For thus says the Lord of hosts: “Cut down her trees, and build a rampart around Jerusalem. This is the city of visitation! Every kind of false claim is in her midst.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku sassare itatuwan ku tula ƙasa kewaye da Urushalima. Dole a hukunta wannan birni; saboda ya cika da zalunci.
7 Just as a cistern makes its water cold, so has she made her wickedness cold. Iniquity and devastation will be heard in her; sickness and wounds will be ever before me.
Kamar yadda rijiya takan ba da ruwarta, haka birnin yake da muguntarsa. Ana jin labarin rikici da hallaka a cikinsa; ciwonsa da mikinsa kullum suna a gabana.
8 O Jerusalem, accept instruction, lest perhaps my soul may withdraw from you; lest perhaps I may set you in a desert, in an uninhabitable land.”
Ki ji gargaɗi, ya Urushalima, ko kuwa in juya daga gare ki in mai da ƙasarki kufai don kada wani ya zauna a cikinta.”
9 Thus says the Lord of hosts: “They will gather the remnant of Israel, even as a single cluster of grapes is gathered from a vine. Direct your hand, as a grape-gatherer directs his hand to the basket.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Bari su yi kalan raguwar Isra’ila a yi kalan sarai yadda ake yi wa inabi; ka sāke miƙa hannunka a kan rassan, kamar mai tattara inabi.”
10 To whom should I speak, and to whom should I testify, so as to be heard? Behold, their ears are uncircumcised, and so they are unable to hear. Behold, for them, the word of the Lord has become a disgrace. And so they will not accept it.
Ga wa zan yi magana in kuma gargaɗar? Wa zai saurare ni? Kunnuwansu sun toshe don kada su ji. Maganar Ubangiji ta zama abin zargi a gare su; ba sa jin daɗinta.
11 For this reason, I have been filled with the fury of the Lord. I labor to bear it. Let it be poured out upon the child outside, or upon a group of young men meeting together. For a man will be taken captive with a woman, an elder will be taken captive with one who is full of days.
Amma ina cike da fushin Ubangiji, kuma ba na iya kannewa. “Ka kwararo shi a kan yara a titi da kuma a kan samarin da suka tattaru; za a kama miji da mata a cikinsa, tsofaffi da suka tsufa tukub.
12 And their houses will be given over to others, with both their lands and their wives. For I will extend my hand over the inhabitants of the earth, says the Lord.
Za a ba da gidajensu ga waɗansu, tare da gonakinsu da matansu, sa’ad da na miƙa hannuna gāba da waɗanda suke zama a ƙasar,” in ji Ubangiji.
13 Certainly, from the least of them even to the greatest, all of them practice greed. And from the prophet even to the priest, all of them act with deceit.
“Daga ƙarami zuwa babba, dukansu masu haɗama ne don riba; har da annabawa da firistoci, dukansu suna aikata rashin gaskiya.
14 And they healed the destruction of the daughter of my people with disgrace, by saying: ‘Peace, peace.’ And there was no peace.
Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali kuwa ba lafiya.
15 They were confounded, because they committed an abomination. Or rather, they were not confounded with shame, because they did not know how to blush. For this reason, they will fall among those who are being destroyed. In the time of their visitation, they will fall, says the Lord.”
Suna jin kunyar halinsu na banƙyama? A’a, ba sa jin kunya sam; ba su ma san yadda za su soke kai ba. Saboda haka za su fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za a hamɓarar da su sa’ad da na hukunta su,” in ji Ubangiji.
16 Thus says the Lord: “Stand above the ways, and see and ask, about the ancient paths, as to which is the good way, and then walk in it. And you will find refreshment for your souls. But they said: ‘We will not walk.’
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba; ku nemi hanyoyin dā, ku tambaya inda hanyar mai kyau take, ku yi tafiya a kanta, za ku kuwa sami hutu wa rayukanku. Amma kun ce, ‘Ba za mu bi ta ba.’
17 And I appointed watchers over you, saying: ‘Listen for the sound of the trumpet.’ And they said: ‘We will not listen.’
Na naɗa muku masu tsaro a kanku na kuma ce, ‘Ku saurari karan ƙaho!’ Amma kuka ce, ‘Ba za mu saurara ba.’
18 For this reason, hear, O Gentiles, and know, O congregation, how much I will do to them.
Saboda haka ku, ya al’ummai; ku lura Ya shaidu, abin da zai faru da su.
19 Hear, O earth! Behold, I will lead evils over this people, as the fruits of their own thoughts. For they have not listened to my words, and they have cast aside my law.
Ki ji, ya duniya. Zan kawo masifa a kan waɗannan mutane, sakayyar ƙulle-ƙullensu, domin ba su saurari maganata ba suka kuma ƙi dokata.
20 For what reason are you bringing me frankincense from Sheba, and sweet smelling reeds from a far away land? Your holocausts are not acceptable, and your sacrifices are not pleasing to me.”
Babu riba a kawo mini turare daga Sheba ko rake mai zaƙi daga ƙasa mai nisa? Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa ba; ba na jin daɗin sadakokinku.”
21 Therefore, thus says the Lord: “Behold I will bring this people to utter ruin, and they will fall, with their fathers and sons; neighbor and relative will perish together.”
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Zan sa abin tuntuɓe gaban mutanena. Mahaifi da’ya’yansa maza za su yi tuntuɓe a kan juna; maƙwabci da abokansa za su hallaka.”
22 Thus says the Lord: “Behold, a people is coming from the land of the north, and a great nation will rise up from the ends of the earth.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Duba, sojoji suna zuwa daga ƙasar arewa; babbar al’umma ce ta yunƙuro daga iyakokin duniya.
23 They will take hold of arrow and shield. They are cruel, and they will not take pity. Their voice will roar like the ocean. And they will climb upon horses, for they have been prepared like men for battle, against you, O daughter of Zion.
Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne kuma marasa tausayi. Motsinsu kamar ƙugin teku ne yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa a jere kamar wanda ya yi shirin yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Sihiyona.”
24 ‘We have heard of their fame. Our hands have become weakened. Tribulation has overtaken us, like the pains of a woman giving birth.’
Mun ji labari a kansu, hannuwanmu kuwa suka yi laƙwas. Azaba ta kama mu, zafi kamar na mace mai naƙuda.
25 Do not choose to go out into the fields, and you should not walk along the roadway. For the sword and the terror of the enemy is on every side.
Kada ku fita zuwa gonaki ko ku yi tafiya a hanyoyi, gama abokin gāba yana da takobi, kuma akwai razana ko’ina.
26 Wrap yourself in haircloth, O daughter of my people. And sprinkle yourself with ashes. Make a mourning for yourself, as for an only son, a bitter lamentation: ‘for the destroyer will overwhelm us suddenly.’
Ya mutanena, ku sanya tufafin makoki ku yi birgima a toka; ku yi kuka mai zafi irin wanda akan yi wa ɗa tilo, gama nan da nan mai hallakarwa zai auko mana.
27 I have presented you as a strong tester among my people. And you will test and know their way.
“Na maishe ka mai jarrabawar ƙarfe mutanena ne kuwa ƙarfen, don ka lura ka kuma gwada hanyoyinsu.
28 All these leaders who are turning away and walking deceitfully, they are brass and iron; they have all been corrupted.
Su duka masu taurinkai ne,’yan tawaye, suna yawo suna baza jita-jita. Su tagulla ne da ƙarfe; dukansu lalatattu ne.
29 The bellows has failed; the lead has been consumed by fire; the molten metal was melted to no purpose. For their wickedness has not been consumed.
Mazuga yana zuga da ƙarfi don yă ƙone dalma da wuta, amma tacewa yana tafiya a banza; ba a fitar da mugaye.
30 Call them: ‘Rejected silver.’ For the Lord has cast them aside.”
Ana ce da su azurfar da aka ƙi, gama Ubangiji ya ƙi su.”

< Jeremiah 6 >