< Jeremiah 45 >

1 The word that Jeremiah the prophet spoke to Baruch, the son of Neriah, when he had written these words in a book, from the mouth of Jeremiah, in the fourth year of Jehoiakim, the son of Josiah, the king of Judah, saying:
Ga abin da Irmiya annabi ya faɗa wa Baruk ɗan Neriya a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, bayan Baruk ya rubuta maganar da Irmiya ya shibta masa a kan littafi cewa,
2 “Thus says the Lord, the God of Israel, to you, Baruch:
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana ce maka, Baruk.
3 You have said: ‘Woe to me, a wretched man! For the Lord has added sorrow to my sorrow. I have labored in my groaning, and I have not found rest.’
Ka ce, ‘Kaitona! Ubangiji ya ƙara baƙin ciki da wahalata; na gaji da nishe-nishe ban kuma huta ba.’”
4 Thus says the Lord: So shall you say to him: Behold, those whom I have built up, I destroy, and those whom I have planted, I uproot, even this entire land.
Ubangiji ya ce, “Ka faɗa masa wannan, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan rushe abin da na gina in kuma tumɓuke abin da na dasa, a duk fāɗin ƙasar.
5 And are you seeking great things for yourself? Do not choose to seek them. For behold, I will lead evil over all that is flesh, says the Lord. But I will give your life to you unto salvation, in every place, wherever you may travel.”
Ya kamata ka nemi manyan abubuwa wa kanka? Kada ka neme su. Gama zan aukar da masifa a kan dukan mutane, in ji Ubangiji, amma duk inda ka tafi zan bar ka ka kuɓutar da ranka.’”

< Jeremiah 45 >