< Jeremiah 4 >

1 “O Israel, if you would return, says the Lord, then be converted to me. If you remove your offense from before my face, then you will not be shaken.
“In za ka komo, ya Isra’ila, ka komo gare ni,” in ji Ubangiji. “In ka kau da gumakanka masu banƙyama daga gabana ba ka ƙara karkace ba,
2 And you will swear, ‘As the Lord lives,’ in truth and in judgment and in justice.” And the Gentiles will bless him, and they will praise him.
kuma in cikin gaskiya da adalci ka rantse, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ to al’ummai za su sami albarka ta wurinsa kuma a cikinsa za su ɗaukaka.”
3 For thus says the Lord to the men of Judah and of Jerusalem: “Break new ground, and do not choose to sow upon thorns.
Ga abin da Ubangiji yana ce wa mutanen Yahuda da kuma na Urushalima. “Ku nome ƙasarku kuma kada ku yi shuka cikin ƙayayyuwa.
4 Be circumcised to the Lord, and take away the foreskins from your hearts, O men of Judah, O inhabitants of Jerusalem. Otherwise my indignation may burst forth and flare up like a fire. And then there will be no one who can extinguish it, because of the wickedness of your thoughts.
Ku yi wa kanku kaciya ga Ubangiji ku yi wa zukatanku kaciya, ku mutanen Yahuda da mutanen Urushalima, in ba haka ba hasalata za tă sauko ta ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci ba wanda zai kashe ta.
5 Declare it in Judah, and make it known in Jerusalem! Speak out and sound the trumpet in the land! Cry out strongly and say: ‘Gather yourselves! And let us go forth to fortified cities!’
“Ku yi shela a Yahuda ku kuma furta a Urushalima ku ce, ‘Ku busa ƙaho a ko’ina a ƙasar!’ Ku tā da murya da ƙarfi ku ce, ‘Ku tattaru! Bari mu gudu zuwa birane masu katanga!’
6 Lift up a standard in Zion. Be strengthened! Do not choose to stand still. For I am bringing an evil from the north, with great destruction.
Ku tā da tuta don zuwa Sihiyona! Ku gudu ku nemi mafaka ba tare da jinkiri ba! Gama ina kawowa masifa daga arewa, mummunan hallaka kuwa.”
7 The lion has ascended from his den, and the pillager of the nations has lifted himself up. He has gone forth from his place, so that he may set your land in desolation. Your cities will be laid waste, remaining without an inhabitant.
Zaki ya fito daga ruƙuƙinsa; mai hallakarwar al’ummai ya kama hanya. Ya bar wurinsa don yă lalace ƙasarku. Garuruwanku za su zama kufai babu mazauna.
8 Concerning this, wrap yourselves in haircloth, mourn and wail: ‘For the wrath of the fury of the Lord has not been turned away from us.’
Saboda haka ku yafa tufafin makoki, ku yi makoki da kuka, gama fushin Ubangiji bai juye daga gare mu ba.
9 And this shall be in that day, says the Lord: The heart of the king will perish, with the heart of the princes. And the priests will be stupefied, and the prophets will be in consternation.”
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “sarki da shugabanni za su fid da zuciya, firistoci za su razana, annabawa kuma za su yi mamaki.”
10 And I said: “Alas, alas, alas, O Lord God! Could it be that you have deceived this people and Jerusalem, saying: ‘Peace shall be yours,’ while, behold, the sword reaches even to the soul?”
Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka, yaya ka ruɗi mutanen nan da kuma Urushalima gaba ɗaya haka ta wurin cewa, ‘Za ku zauna lafiya,’ sa’ad da takobi yana a maƙogwaronmu.”
11 “In that time, it will be said to this people and to Jerusalem: ‘A burning wind is in the ways that are in the desert, along the way of the daughter of my people, but not to winnow and not to cleanse.’
A lokacin za a faɗa wa mutanen nan da kuma Urushalima cewa, “Iska mai zafi daga tuddan hamada za tă hura zuwa wajen mutanena, amma ba don ta sheƙe ko ta rairaye; ba;
12 A full spirit from these places will come to me. And now I will speak my judgments over them.
iska mafificin ƙarfi da ta fito daga gare ni. Yanzu na zartar da hukuncina a kansu.”
13 Behold, he will ascend like a cloud, and his chariot will ascend like a tempest. His horses are swifter than eagles. ‘Woe to us! For we are being devastated!’
Duba! Yana zuwa kamar gizagizai, kekunan yaƙinsa suna zuwa kamar guguwa, dawakansa sun fi gaggafa sauri. Kaiton mu! Mun shiga uku!
14 Wash your heart from malice, O Jerusalem, so that you may be saved. How long will harmful thoughts abide in you?
Ya Urushalima, ki wanke mugunta daga zuciyarki ki sami ceto. Har yaushe za ki zauna riƙe da mugayen tunani?
15 For there is a voice, of someone announcing from Dan, and he is making known the idol from mount Ephraim.
Murya ta shela daga Dan, tana furtawa masifa daga tuddan Efraim.
16 Say to the nations: ‘Behold, it has been heard in Jerusalem! Guardians are coming from a far away land, to utter their voice against the cities of Judah.’
“A faɗa wa al’ummai wannan, a furta wannan game Urushalima. ‘Sojoji masu ƙawanya suna zuwa daga ƙasa mai nisa, suna tā da kirarin yaƙi a kan biranen Yahuda.
17 They have been stationed over her, like the guardians of fields, all around. For she has provoked me to wrath, says the Lord.
Sun kewaye ta kamar masu gadin fili, domin ta yi mini tawaye,’” in ji Ubangiji.
18 Your ways and your thoughts have brought these things upon you. This is your own wickedness. And it is bitter, because it has touched your heart.
“Halinki da ayyukanki sun kawo wannan a kanki. Hukuncinki ke nan. Yana da ɗaci! Ya soke ki har zuciyarki!”
19 I am afflicted in my heart, in my heart. The senses of my heart have been stirred up within me. I will not remain silent. For my soul has heard the voice of the trumpet, the clamor of the battle.
Azabana, azabana! Ina birgima cikin zafi. Azabana, azabar zuciyata! Zuciyata yana bugu a cikina, Ba zan yi shiru ba. Gama na ji karan ƙaho; na ji kirarin yaƙi.
20 Destruction upon destruction has been called forth. And the entire earth has been devastated. My tabernacles have been destroyed suddenly, and my tents in an instant.
Masifa kan masifa; dukan ƙasar ta zama kufai. Cikin ɗan lokaci aka rurrushe tentuna nawa, mafakata ba zato.
21 How long shall I watch those who are fleeing, and listen to the voice of the trumpet?
Har yaushe zan dubi tutar yaƙi in kuma ji karar ƙaho?
22 For my foolish people have not known me. They are foolish and mad sons. They are clever in doing evil, but they do not know how to do good.
“Mutanena wawaye ne; ba su san ni ba. Su’ya’ya ne marasa azanci; ba su da fahimi. Suna da dabarar aikata mugunta; ba su san yadda za su aikata alheri ba.”
23 I gazed upon the earth, and behold, it was empty and brought to nothing. And I gazed upon the heavens, but there was no light in them.
Na dubi duniya, na ga cewa marar siffa ce babu kome; sammai kuma, haskensu ya tafi.
24 I watched the mountains, and behold, they trembled, and all the hills were shaken.
Na dubi duwatsu, sai na ga suna makyarkyata; dukan tuddai kuwa suna lilo.
25 I looked, and there was no man. And all the flying things of the air had gone away.
Na duba, sai na ga ba kowa; kowane tsuntsu a sarari da ya tsere.
26 I gazed, and behold, Carmel was a desert, and all its cities were destroyed before the face of the Lord, and before the face of the wrath of his fury.”
Na duba, sai na ga ƙasa mai amfani ta zama hamada; dukan garuruwanta sun zama kufai a gaban Ubangiji, a gaban zafin fushinsa.
27 For thus says the Lord: “All the earth will be desolate, but I will not yet bring about its consummation.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dukan ƙasar za tă zama kufai, ko da yake ba zan hallaka ta gaba ɗaya ba.
28 The earth will mourn, and the heavens will lament from above. For I have spoken, I have decided, and I have not regretted. Neither will I be turned away from it.
Saboda haka duniya za tă yi kuka sammai a bisa kuma za su yi duhu, domin na yi magana kuma ba zan fasa ba, na yanke shawara ba kuwa zan janye ba.”
29 Before the voice of the horsemen and of those who send forth arrows, the entire city has fled. They have entered steep places, and they have ascended the cliffs. All of the cities have been abandoned, and no man lives within them.
Da jin motsin mahayan dawakai da maharba kowane gari ya ruga da gudu. Waɗansu suka shiga kurmi; waɗansu suka hau cikin duwatsu. Dukan garuruwan sun fashe tas; babu wani da yake zama a ciki.
30 So then, when you have been devastated, what will you do? Though you will clothe yourself with scarlet, though you will adorn yourself with a gold necklace and tint your eyes with cosmetics, you will be dressing yourself up in vain. Your lovers have spurned you; they will be seeking your life.
Me kike yi, ya wadda aka ragargaza? Me ya sa kika sanya mulufi kika sa kayan adon zinariya? Me ya sa kika sa wa idanunki tozali? Kin yi kwalliyarki a banza. Masoyanki sun bar ki; suna neman ranki.
31 For I have heard a voice, like that of a woman giving birth, during the difficulties of labor. It is the voice of the daughter of Zion, dying, extending her hands: ‘Woe to me! For my soul is failing because of those who have been slain!’”
Na ji kuka kamar na mace mai naƙuda, nishi kamar na wadda take haihuwa ɗanta na fari, kukan Diyar Sihiyona tana haki, da ƙyar take numfashi, tana miƙa hannuwanta tana cewa, “Wayyo ni kaina! Na suma; an ba da raina ga masu kisana.”

< Jeremiah 4 >