< Jeremiah 39 >

1 In the ninth year of Zedekiah, the king of Judah, in the tenth month, Nebuchadnezzar, the king of Babylon, came to Jerusalem, with his entire army, and they besieged it.
A shekara ta tara ta Zedekiya sarkin Yahuda, a wata na goma, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fita yaƙi da Urushalima da dukan sojojinsa ya kuma yi mata ƙawanya.
2 Then, in the eleventh year of Zedekiah, in the fourth month, on the fifth of the month, the city was opened.
A rana ta tara ga watan huɗu a shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya, sai aka huda katanga.
3 And all the rulers of the king of Babylon entered and were seated at the middle gate: Nergal-Sharezer, the priest of Nebo, Sarsechim, the chief eunuch, Nergal-Sharezer, the chief magi, and all the other rulers of the king of Babylon.
Sa’an nan dukan fadawan sarkin Babilon suka shiga suka zazzauna a Ƙofar Tsakiya. Wato, Nergal-Sharezer na Samgar-Nebo, Sarsekim wani babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da dukan sauran fadawan sarkin Babilon.
4 And when Zedekiah, the king of Judah, with all the men of war, had seen them, they fled. And they departed from the city at night, by way of the king’s garden, and through the gate which was between the two walls. And they departed along the way of the desert.
Sa’ad da Zedekiya sarkin Yahuda da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu; suka bar birnin da dare ta hanyar lambun sarki, ta ƙofar da take tsakanin katanga biyu, suka nufi waje Araba.
5 But the army of the Chaldeans pursued them. And they overtook Zedekiah in the plain of the desert of Jericho. And having captured him, they led him to Nebuchadnezzar, the king of Babylon, at Riblah, which is in the land of Hamath. And he declared a judgment against him
Amma sojojin Babiloniyawa suka bi su, suka ci wa Zedekiya a filayen Yeriko. Suka kama shi suka kai shi wurin Nebukadnezzar a Ribla a ƙasar Hamat, inda aka yanke masa hukunci.
6 And the king of Babylon killed the sons of Zedekiah, at Riblah, before his eyes. And the king of Babylon killed all the nobles of Judah.
A can Ribla sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idanunsa aka kuma kashe dukan manyan mutanen Yahuda.
7 Also, he plucked out the eyes of Zedekiah. And he bound him with fetters, to be led away to Babylon.
Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya ya kuma buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babilon.
8 Also, the Chaldeans burned the house of the king and the house of the people with fire, and they overturned the wall of Jerusalem.
Sai Babiloniyawa suka cinna wa fadar da kuma gidajen mutane wuta suka farfasa katangar Urushalima.
9 And Nebuzaradan, the leader of the military, carried away captive to Babylon the remnant of the people who had remained in the city, and the fugitives who had fled to him, and all the rest of the people who had remained.
Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya kwashi mutanen da suka rage a birnin zuwa zaman bauta a Babilon, tare da waɗanda suka riga suka tafi wurinsa, da kuma sauran mutanen.
10 And Nebuzaradan, the leader of the military, released some of the poor people, those who had almost nothing, into the land of Judah. And he gave them vineyards and cisterns in that day.
Amma Nebuzaradan shugaban matsaran ya bar waɗansu matalauta a ƙasar Yahuda, su da ba su da kome; a lokacin kuwa ya ba su gonakin inabi da kuma filaye.
11 Now Nebuchadnezzar, the king of Babylon, had instructed Nebuzaradan, the leader of the military, about Jeremiah, saying:
To, fa, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ba da wannan umarnai game da Irmiya ta wurin Nebuzaradan shugaban matsaran sarki cewa,
12 “Take him, and set your eyes on him, and you shall do no harm to him at all. But as he is willing, so shall you do with him.”
“Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”
13 Therefore, Nebuzaradan, the leader of the military, sent, and Nebushazban, the chief eunuch, and Nergal-Sharezer, the chief magi, and all the nobles of the king of Babylon sent,
Saboda haka Nebuzaradan shugaban matsara, Nebushazban babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da sauran hafsoshin sarkin Babilon
14 and they took Jeremiah from the vestibule of the prison, and they delivered him to Gedaliah, the son of Ahikam, the son of Shaphan, so that he could enter a house and live among the people.
suka aika aka kawo Irmiya daga filin matsar. Suka miƙa shi ga Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, don yă kai shi gidansa. Saboda haka ya zauna a can a cikin mutanensa.
15 But the word of the Lord had come to Jeremiah, when he had been confined to the vestibule of the prison, saying: “Go, and speak to Ebedmelech, the Ethiopian, saying:
Yayinda aka kulle Irmiya a sansanin matsara, maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
16 Thus says the Lord of hosts, the God of Israel: Behold, I will bring my words over this city for evil, and not for good; and they shall be in your sight in that day.
“Tafi ka faɗa wa Ebed-Melek mutumin Kush, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ina gab da cika maganata a kan wannan birni ta wurin masifa, ba wadata ba. A lokacin za tă cika a idanunka.
17 And I will free you in that day, says the Lord. And you will not be delivered into the hands of the men whom you dread.
Amma zan kuɓutar da kai a wannan rana, in ji Ubangiji; ba zan ba da kai ga waɗanda kake tsoronsu ba.
18 But when delivering, I will free you. And you will not fall by the sword. Instead, your life will be saved for you, because you had faith in me, says the Lord.”
Zan cece ka; ba za ka mutu ta wurin takobi ba amma za ka tsira da ranka, domin ka dogara gare ni, in ji Ubangiji.’”

< Jeremiah 39 >