< Jeremiah 36 >

1 And it happened in the fourth year of Jehoiakim, the son of Josiah, the king of Judah: it happened that this word came to Jeremiah from the Lord, saying:
A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
2 “Take the volume of a book, and you shall write in it all the words that I have spoken to you against Israel and Judah, and against all the nations, from the day when I first spoke to you, from the days of Josiah, even to this day.
“Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
3 Perhaps it may be that the house of Judah, upon hearing all the evils that I have decided to do to them, may return, each one from his wicked way, and then I will forgive their iniquity and their sin.”
Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
4 Therefore, Jeremiah called Baruch, the son of Neriah, and Baruch wrote, from the mouth of Jeremiah, all the words of the Lord, which he had spoken to him, in the volume of a book.
Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
5 And Jeremiah instructed Baruch, saying: “I am confined, and so I am unable to enter into the house of the Lord.
Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
6 Therefore, you shall enter and read from the volume, in which you have written from my mouth the words of the Lord, in the hearing of the people in the house of the Lord on the day of the fast. Moreover, you shall also read them in the hearing of all those of Judah who are arriving from their cities.
Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
7 Perhaps it may happen that they pray in the sight of the Lord, and each one may return from his wicked way. For great is the fury and indignation that the Lord has declared against this people.”
Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
8 And Baruch, the son of Neriah, acted in accord with all that Jeremiah, the prophet, had instructed him, reading from the volume the words of the Lord, in the house of the Lord.
Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
9 And it happened that, in the fifth year of Jehoiakim, the son of Josiah, the king of Judah, in the ninth month, they proclaimed a fast, in the sight of the Lord, to all the people in Jerusalem, and to the entire multitude which had flowed together, from the cities of Judah, into Jerusalem.
A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
10 And Baruch read from the volume the words of Jeremiah in the house of the Lord, at the treasury of Gemariah, the son of Shaphan, the scribe, in the upper vestibule, at the entrance to the new gate of the house of the Lord, in the hearing of all the people.
Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
11 And when Micaiah, the son of Gemariah, the son of Shaphan, had heard all the words of the Lord from the book,
Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
12 he descended to the house of the king, to the treasury of the scribe. And behold, all the leaders were sitting there: Elishama, the scribe, and Delaiah, the son of Shemaiah, and Elnathan, the son of Achbor, and Gemariah, the son of Shaphan, and Zedekiah, the son of Hananiah, and all the leaders.
sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
13 And Micaiah announced to them all the words that he had heard when Baruch read from the volume to the ears of the people.
Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
14 And so, all the leaders sent Jehudi, the son of Nethaniah, the son of Shelemiah, the son of Cushi, to Baruch, saying, “Take in your hand the volume, from which you have read in the hearing of the people, and come.” Therefore, Baruch, the son of Neriah, took the volume in his hand, and he went to them.
sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
15 And they said to him, “Sit and read these things in our hearing.” And Baruch read in their hearing.
Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
16 Therefore, when they had heard all the words, each one looked at his neighbor in astonishment, and they said to Baruch: “We ought to report all these words to the king.”
Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
17 And they questioned him, saying, “Describe to us how you wrote all these words from his mouth.”
Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
18 Then Baruch said to them: “He was speaking with his mouth, as if reading to me. And I wrote in a volume with ink.”
Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
19 And the leaders said to Baruch: “Go away and hide, you and Jeremiah, and let no one know where you are.”
Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
20 And they entered to the king, in the court. Furthermore, they stored the volume in the treasury of Elishama, the scribe. And they announced all the words in the hearing of the king.
Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
21 And the king sent Jehudi to take the volume. And bringing it from the treasury of Elishama, the scribe, he read it in the hearing of the king and of all the leaders who were standing around the king.
Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
22 Now the king was sitting in the winter house, in the ninth month. And there was a hearth placed before him, filled with burning coals.
A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
23 And when Jehudi had read three or four pages, he cut it with a small knife, and he threw it into the fire which was upon the hearth, until the entire volume was consumed by the fire which was upon the hearth.
Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
24 And the king and all his servants, who had heard all these words, were not afraid, and they did not rend their garments.
Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
25 Yet truly, Elnathan, and Delaiah, and Gemariah contradicted the king, so that he might not burn the book. But he did not listen to them.
Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
26 And the king instructed Jerahmeel, the son of Amelech, and Seraiah, the son of Azriel, and Shelemiah, the son of Abdeel, so that they would apprehend Baruch, the scribe, and Jeremiah, the prophet. But the Lord concealed them.
A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
27 And after the king had burned the volume and the words that Baruch had written from the mouth of Jeremiah, the word of the Lord came to Jeremiah, the prophet, saying:
Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
28 “Again, take another volume and write in it all the former words, which were in the first volume that Jehoiakim, the king of Judah, has burned.
“Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
29 And you shall say to Jehoiakim, the king of Judah: Thus says the Lord: You have burned that volume, saying: ‘Why have you written in it, announcing that the king of Babylon will advance quickly, and will devastate this land, and will cause both man and beast to cease from it?’
Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
30 Because of this, thus says the Lord against Jehoiakim, the king of Judah: There will be, from him, no one who may sit upon the throne of David. And his dead body shall be cast out: to the heat by day, and to the frost by night.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
31 And I will visit against him, and against his offspring, and against his servants for their iniquities. And I will lead over them, and over the inhabitants of Jerusalem, and over the men of Judah, all the evil that I have declared against them, for they have not listened.”
Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
32 Then Jeremiah took up another volume, and he gave it to Baruch, the son of Neriah, the scribe, who wrote in it, from the mouth of Jeremiah, all the words of the book that Jehoiakim, the king of Judah, had burned with fire. And moreover, there were many more words added than there had been before.
Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.

< Jeremiah 36 >