< Jeremiah 32 >

1 The word that came to Jeremiah from the Lord in the tenth year of Zedekiah, the king of Judah. The same is the eighteenth year of Nebuchadnezzar.
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji a shekara ta goma ta Zedekiya sarkin Yahuda, wanda ya kasance shekara ta goma sha takwas ta Nebukadnezzar.
2 It was then that the army of the king of Babylon besieged Jerusalem. And Jeremiah, the prophet, was confined to the atrium of the prison, which was in the house of the king of Judah.
Sojojin sarkin Babilon a lokacin suna ƙawanya wa Urushalima annabi Irmiya kuwa yana a tsare a sansanin matsara a fadar Yahuda.
3 For Zedekiah, the king of Judah, had confined him, saying: “Why do you make predictions, saying: ‘Thus says the Lord: Behold, I will give this city into the hand of the king of Babylon, and he will capture it?
Zedekiya sarkin Yahuda fa ya sa shi a kurkuku yana cewa, “Don me kake yin annabci? Ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa cinye ta.
4 And Zedekiah, the king of Judah, will not escape from the hand of the Chaldeans. Instead, he will be delivered into the hands of the king of Babylon. And he will speak to him, mouth to mouth, and he will see him, eye to eye.
Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kuɓuta daga hannuwan Babiloniyawa ba amma tabbatacce za a ba da shi ga sarkin Babilon, zai kuwa yi masa magana fuska da fuska ya kuma gan shi da idanunsa.
5 And he will lead Zedekiah to Babylon. And he will be there until I visit him, says the Lord. So then, if you contend against the Chaldeans, you will have no success.’”
Zai kai Zedekiya Babilon, inda zai zauna har sai ya magance shi, in ji Ubangiji. In ka yi yaƙi da Babiloniyawa, ba za ka yi nasara ba.’”
6 And Jeremiah said: “The word of the Lord came to me, saying:
Irmiya ya ce, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
7 Behold, Hanamel, the son of Shallum, your cousin, will come to you, saying: ‘Buy for yourself my field, which is in Anathoth. For it is your right, as next of kin, to buy it.’
Hananel ɗan Shallum ɗan’uwan mahaifinka zai zo wurinka ya ce, ‘Saya filina a Anatot, domin a matsayinka na dangi na kurkusa hakkinka ne kuma kai ya wajaba ka saye shi.’
8 And in accord with the word of the Lord, Hanamel, the son of my uncle, came to me, to the entrance of the prison, and he said to me: ‘Take possession of my field, which is in Anathoth in the land of Benjamin. For the right of inheritance is yours, and as the next of kin you may possess it.’ Then I understood that this was the word of the Lord.
“Sa’an nan, kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa, sai ga Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina ya zo wurina a sansanin matsara ya ce, ‘Saya filina a Anatot a yankin Benyamin. Da yake hakkinka ne ka fanshe shi ka kuma mallake shi, ka sayo shi wa kanka.’ “Sai na gane cewa wannan maganar Ubangiji ce;
9 And I bought the field, which is in Anathoth, from Hanamel, the son of my uncle. And I weighed out the money to him, seven small coins and ten pieces of silver.
saboda haka sai na saye filin a Anatot daga hannun Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina na kuma auna masa shekel goma sha bakwai na azurfa.
10 And I wrote it in a book and signed it, and I summoned witnesses. And I weighed out the silver on a scale.
Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna shekel a ma’auni.
11 And I received the signed deed of possession, and the stipulations, and the ratifications, with the exterior seals.
Na ɗauki takardar ciniki, takardar da aka rubuta sharuɗan a ciki, da kuma takardar da ba a liƙe ba,
12 And I gave the deed of possession to Baruch, the son of Neriah, the son of Mahseiah, in the sight of Hanamel, the son of my uncle, in the sight of the witnesses who had been recorded in the book of the purchase, and in the sight of all the Jews who were sitting in the atrium of the prison.
na kuma ba wa Baruk ɗan Neriya, ɗan Masehiya, wannan takarda a gaban Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina da kuma a gaban shaidun da suka sa hannu a takardan ciniki da kuma a gaban dukan Yahudawan da suke zaune a sansanin matsaran.
13 And I instructed Baruch, in their sight, saying:
“A gabansu na yi wa Baruk waɗannan umarnai cewa,
14 Thus says the Lord of hosts, the God of Israel: ‘Take these writings, this sealed deed of purchase, and this deed which is open, and place them in an earthen vessel, so that they will be preserved for many days.’
‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka ɗauki waɗannan takardun ciniki, wanda aka liƙe da wanda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tulun yumɓu don kada su lalace.
15 For thus says the Lord of hosts, the God of Israel: ‘Houses, and fields, and vineyards will be possessed still, in this land.’
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa za a sāke saye gidaje, filaye da gonakin inabi a wannan ƙasa.’
16 And after I had delivered the deed of possession to Baruch, the son of Neri, I prayed to the Lord, saying:
“Bayan na ba da takardun ciniki ga Baruk ɗan Neriya, sai na yi addu’a ga Ubangiji na ce,
17 Alas, alas, alas, O Lord God! Behold, you have made heaven and earth, by your great strength and by your outstretched arm. No word is difficult for you.
“A, Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka mai girma da kuma hannunka mai iko. Ba abin da ya gagare ka.
18 You act with mercy a thousand-fold, but you repay the iniquity of the fathers into the sinews of their sons after them. The Lord of hosts is your name: most strong, great, and powerful!
Kakan nuna ƙauna ga dubbai amma kakan hukunta’ya’ya saboda laifin ubanninsu a bayansu. Ya mai girma da kuma Allah mai iko, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki,
19 You are great in counsel and incomprehensible in thought. Your eyes are open upon all the ways of the sons of Adam, so that you may repay each one according to his ways and according to the fruit of his intentions.
manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
20 You caused signs and portents in the land of Egypt, and in Israel, and among men, even until this day. And you have made a name for yourself, just as in this day.
Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.
21 And you have led your people Israel away from the land of Egypt, with signs and portents, and with a robust hand and an outstretched arm, and with great terror.
Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.
22 And you have given them this land, which you swore, to their fathers, that you would give to them, a land flowing with milk and honey.
Ka ba su wannan ƙasa da ka rantse za ka ba wa kakanni kakanninsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
23 And they entered it and possessed it. But they did not obey your voice, and they did not walk in your law. And they did not do all of the things that you commanded them to do. And so, all of these evils have happened to them.
Suka shiga suka mallake ta, amma ba su yi maka biyayya ba, ba su kuma bi dokarka ba; ba su yi abin da ka umarce su ba. Saboda haka ka kawo masifa a kansu.
24 Behold, fortifications were built against the city, so as to capture it. And the city was given into the hands of the Chaldeans, who fight against it, before the face of the sword, and of famine, and of pestilence. And what you have spoken has occurred, just as you yourself discern.
“Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
25 So why, O Lord God, are you saying to me: ‘Buy a field with money, and summon witnesses,’ while the city is being given into the hands of the Chaldeans?”
Ko da yake za a ba da birnin ga Babiloniyawa, kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka ce mini, ‘Saye fili da azurfa ka kuma sa a shaida cinikin.’”
26 And the word of the Lord came to Jeremiah, saying:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
27 “Behold, I am the Lord God; I am above all flesh. Can any word be difficult for me?
“Ni ne Ubangiji Allah na dukan’yan adam. Akwai wani abin da ya gagare ni?
28 Therefore, thus says the Lord: Behold, I will deliver this city into the hands of the Chaldeans, and into the hands of the king of Babylon, and they will capture it.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga Babiloniyawa da kuma ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, wanda zai yaƙe ta.
29 And the Chaldeans fighting against this city will advance, and set fire to it, and burn it, along with the houses on whose roofs they were offering sacrifice to Baal and were pouring out libations to strange gods, so that they provoked me to wrath.
Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
30 For the sons of Israel and the sons of Judah, from their youth, have continually done evil in my eyes. The sons of Israel, even until now, have been provoking me with the work of their hands, says the Lord.
“Mutanen Isra’ila da na Yahuda ba abin da suka yi sai mugunta a gabana daga ƙuruciyarsu; tabbatacce, mutanen Isra’ila ba su yi kome ba sai dai tsokane ni da abin da hannuwansu suka yi, in ji Ubangiji.
31 For this city has been a cause of fury and indignation to me, from the day when they built it, until this day, in which it will be taken away from my sight,
Daga ranar da aka gina ta har zuwa yanzu, wannan birni ta tā da fushina da hasalata da dole a kawar da ita daga gabana.
32 because of all the wickedness of the sons of Israel and the sons of Judah, which they have done, provoking me to wrath, they and their kings, their leaders and their priests and their prophets, the men of Judah and the inhabitants of Jerusalem.
Mutanen Isra’ila da na Yahuda sun tsokane ni ta wurin dukan muguntar da suka aikata su, sarakunansu da fadawansu, firistocinsu da annabawa, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima.
33 And they have turned their backs to me, and not their faces. And though I taught them and instructed them, rising at first light, they were not willing to listen, so that they would receive discipline.
Sun juya mini bayansu ba fuskokinsu ba; ko da yake na koyar da su sau da sau, ba su saurara ko bi horo na ba.
34 And they have placed their idols in the house where my name is invoked, so that they defiled it.
Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.
35 And they have built the exalted places of Baal, which are in the valley of the son of Hinnom, so that they may initiate their sons and their daughters into Molech, though I did not command, nor did it enter into my heart, that they should do this abomination, and so lead Judah into sin.
Sun gina masujadai kan tudu wa Ba’al a Kwarin Ben Hinnom don su miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ga Molek, ko da yake ban taɓa umarce su ba, bai kuma zo mini cewa su yi abin banƙyama irin wannan ba ta haka suka sa Yahuda ya yi zunubi.
36 And now, because of these things, thus says the Lord, the God of Israel, to this city, about which you say that it will be delivered into the hands of the king of Babylon by the sword, and by famine, and by pestilence:
“Kana cewa game da wannan birni, ‘Ta wurin takobi, yunwa da annoba za a ba da shi ga sarkin Babilon’; amma ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa
37 Behold, I will gather them together from all the lands to which I have cast them out in my fury, and in my wrath, and in my great indignation. And I will lead them back to this place, and I will cause them to live in confidence.
tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
38 And they will be my people, and I will be their God.
Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
39 And I will give to them one heart and one way, so that they may fear me all their days, and so that it may be well with them, and with their sons after them.
Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin’ya’yansu a bayansu.
40 And I will form an everlasting covenant with them, and I will not cease to do good for them. And I will put my fear into their heart, so that they do not withdraw from me.
Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
41 And I will rejoice over them, while I do good for them. And I will plant them in this land, in truth, with my whole heart and with my whole soul.
Zan yi farin ciki a yin musu alheri, tabbatacce zan su dasa a wannan ƙasa da dukan zuciyata da dukan raina.
42 For thus says the Lord: Just as I have led over this people all this great evil, so will I lead over them all the good that I am speaking to them now.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, yadda na kawo dukan wannan masifa a kan wannan mutane, haka zan ba su wadatar da na yi musu alkawari.
43 And fields will be possessed in this land, about which you say that it is desolate because there remains neither man nor beast, and because it has been given into the hands of the Chaldeans.
Za a sāke sayi filaye a wannan ƙasa da kuka ce, ‘Kango ce, ba mutane ko dabbobi, gama an ba da ita ga Babiloniyawa.’
44 Fields will be bought for money, and deeds will be written and signed, and witnesses will be summoned, in the land of Benjamin and all around Jerusalem, in the cities of Judah, and in the cities on the mountains, and in the cities on the plains, and in the cities that are toward the south. For I will convert their captivity, says the Lord.”
Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”

< Jeremiah 32 >