< Isaiah 1 >

1 The vision of Isaiah, the son of Amoz, which he saw concerning Judah and Jerusalem, in the days of Uzziah, Joatham, Ahaz, and Hezekiah, kings of Judah.
Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
2 Listen, O heavens, and pay attention, O earth, for the Lord has spoken. I have nurtured and raised children, but they have spurned me.
Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
3 An ox knows his owner, and a donkey knows the manger of his lord, but Israel has not known me, and my people have not understood.
Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
4 Woe to a sinful nation, a people burdened by iniquity, a wicked offspring, accursed children. They have abandoned the Lord. They have blasphemed the Holy One of Israel. They been taken away backwards.
Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
5 For what reason shall I continue to strike you, as you increase transgressions? The entire head is feeble, and the entire heart is grieving.
Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
6 From the sole of the foot, even to the top of the head, there is no soundness within. Wounds and bruises and swelling sores: these are not bandaged, nor treated with medicine, nor soothed with oil.
Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
7 Your land is desolate. Your cities have been set ablaze. Foreigners devour your countryside in your sight, and it will become desolate, as if devastated by enemies.
Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
8 And the daughter of Zion will be left behind, like an arbor in a vineyard, and like a shelter in a cucumber field, and like a city being laid to waste.
An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
9 If the Lord of hosts had not bequeathed us offspring, we would have been like Sodom, and we would have been comparable to Gomorrah.
Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
10 Listen to the Word of the Lord, you leaders of the people of Sodom. Listen closely to the law of our God, O people of Gomorrah.
Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
11 The multitude of your sacrifices, what is that to me, says the Lord? I am full. I do not desire holocausts of rams, nor the fat of fatlings, nor the blood of calves and of lambs and of he-goats.
Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
12 When you approach before my sight, who is it that requires these things from your hands, so that you would walk in my courts?
Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
13 You should no longer offer sacrifice in vain. Incense is an abomination to me. The new moons and the Sabbaths and the other feast days, I will not receive. Your gatherings are iniquitous.
Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
14 My soul hates your days of proclamation and your solemnities. They have become bothersome to me. I labor to endure them.
Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
15 And so, when you extend your hands, I will avert my eyes from you. And when you multiply your prayers, I will not heed you. For your hands are full of blood.
Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
16 Wash, become clean, take away the evil of your intentions from my eyes. Cease to act perversely.
Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
17 Learn to do good. Seek judgment, support the oppressed, judge for the orphan, defend the widow.
Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
18 And then approach and accuse me, says the Lord. Then, if your sins are like scarlet, they shall be made white like snow; and if they are red like vermillion, they shall become white like wool.
Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
19 If you are willing, and you listen to me, then you will eat the good things of the land.
In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
20 But if you are not willing, and you provoke me to anger, then the sword will devour you. For the mouth of the Lord has spoken.
amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
21 How has the faithful city, full of judgment, become a harlot? Justice lived in her, but now murderers.
Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
22 Your silver has turned into dross. Your wine has been mixed with water.
Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
23 Your leaders are unfaithful, the associates of thieves. They all love gifts; they pursue rewards. They do not judge for orphans, and the widow’s case is not brought before them.
Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
24 Because of this, the Lord God of hosts, the Strength of Israel, says: Ah! I will be consoled over my enemies, and I will be vindicated from my adversaries.
Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
25 And I will turn my hand to you. And I will temper your dross unto purity, and I will take away all your tin.
Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
26 And I will restore your judges, so that they will be as before, and your counselors as in times long past. After this, you shall be called the City of the Just, the Faithful City.
Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
27 Zion will be redeemed in judgment, and they will lead her back to justice.
Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
28 And he shall crush the accursed and sinners together. And those who have abandoned the Lord will be consumed.
Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
29 For they shall be confounded because of the idols, to which they have sacrificed. And you shall be ashamed over the gardens that you chose,
“Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
30 when you were like an oak with falling leaves, and like a garden without water.
Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
31 And your strength will be like the embers from stubble, and your work will be like a spark, and both will burn together, and there will be no one to extinguish it.
Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”

< Isaiah 1 >