< Jeremiah 23 >

1 “Woe to the shepherds who scatter and tear apart the sheep of my pasture, says the Lord.
“Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
2 Because of this, thus says the Lord, the God of Israel, to the shepherds who pasture my people: You have scattered my flock, and you have driven them away, and you have not visited them. Behold, I will visit upon you because of your evil pursuits, says the Lord.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
3 And I will gather together the remnant of my flock from the entire earth, from the places to which I had cast them out. And I will return them to their own fields. And they will increase and be multiplied.
“Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
4 And I will raise up shepherds over them, and they will pasture them. They will no longer dread, and they will no longer fear. And no one among their number will be seeking more, says the Lord.
Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
5 Behold, the days are approaching, says the Lord, when I will raise up to David a righteous branch. And a king will reign, and he will be wise. And he will exercise judgment and justice upon the earth.
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
6 In those days, Judah will be saved, and Israel will live in confidence. And this is the name that they will call him: ‘The Lord, our Just One.’
A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
7 Because of this, behold, the days are approaching, says the Lord, when they will no longer say, ‘As the Lord lives, who led the sons of Israel away from the land of Egypt,’
“Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
8 but instead, ‘As the Lord lives, who led away and brought back the offspring of the house of Israel from the land of the north and from the entire earth,’ from the places to which I had cast them out. And they will live in their own land.”
amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
9 To the prophets: “My heart is crushed within me. All my bones are trembling. I have become like an inebriated man, and like a man maddened by wine, before the face of the Lord, and before the face of his holy words.
Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
10 For the earth is full of adulterers! And the earth has mourned before the face of evil talk. The plains of the desert have dried up, and their course has become hazardous, and their firmness has become uneven.”
Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
11 “For both the prophet and the priest have become polluted, and I have found their wickedness within my own house, says the Lord.
“Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
12 For this reason, their way will be like a slippery path in the dark. For they will be impelled forward, and they will fall in it. For I will bring evils over them, in the year of their visitation, says the Lord.
“Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
13 And I have seen the foolishness of the prophets of Samaria. They have prophesied in Baal, and they have deceived my people Israel.
“A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
14 And in the prophets of Jerusalem, I have seen the likeness of adulterers and the path of falsehood. And they have strengthened the hands of the wicked, so that each one would not convert from his malice. They have all become to me like Sodom, and its inhabitants have become like Gomorrah.”
A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
15 Because of this, thus says the Lord of hosts to the prophets: “Behold, I will feed them absinthe, and I will give them gall to drink. For from the prophets of Jerusalem corruption has gone forth over the entire earth.”
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
16 Thus says the Lord of hosts: “Do not choose to listen to the words of the prophets who prophesy to you and deceive you. They speak a vision from their own heart, and not from the mouth of the Lord.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
17 To those who blaspheme me, they say: ‘The Lord has said: You shall have peace.’ And to everyone who walks in the depravity of his own heart, they have said: ‘No evil will overwhelm you.’”
Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
18 For who has been present in the counsel of the Lord, and who has seen and heard his word? Who has considered his word and heard it?
Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
19 Behold, the whirlwind of the Lord’s indignation will go forth, and a tempest will break out; it will overwhelm the head of the impious.
Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
20 The fury of the Lord will not return until it succeeds, and until it completes the plan of his heart. In the last days, you will understand this counsel.
Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
21 “I did not send these prophets, yet they hurry forward. I was not speaking to them, yet they were prophesying.
Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
22 If they had stood in my counsel, and if I had made my words known to my people, certainly I would have turned them away from their evil ways and from their most wicked plans.
Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
23 Do you not realize that I am a God close by, says the Lord, and not a God far away?
“Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
24 If a man is hidden in concealed places, do I not see him, says the Lord? Do I not fill up heaven and earth, says the Lord?
Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
25 I have heard what the prophets have said, prophesying falsehoods in my name, and also saying: ‘I have dreamed! I have dreamed!’
“Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
26 How long will this be in the heart of the prophets who predict what is false, and who prophesy deceptions from their own heart?
Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
27 They want to cause my people to forget my name, by means of their dreams, which each of them describes to his neighbor, just as their fathers forgot my name for the sake of Baal.
Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
28 The prophet who has had a dream, let him describe the dream. And he who receives my word, let him speak my word in truth. For what has the chaff to do with the wheat, says the Lord?
Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
29 Are not my words like a fire, says the Lord, and like a hammer crushing rock?
“Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
30 Therefore, behold: I am against the prophets, says the Lord, who steal my words, each one from his neighbor.
“Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
31 Behold, I am against the prophets, says the Lord, who take up their tongues and say: ‘The Lord says it.’
I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
32 Behold, I am against the prophets, who dream what is false, says the Lord; who explain and so seduce my people with their falsehoods and with their miracles, though I did not send them, nor did I command them. They have offered nothing beneficial to this people, says the Lord.
Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
33 Therefore, if this people, or a prophet, or a priest questions you, saying, ‘What is the burden of the Lord?’ you shall say to them, ‘You are the burden. And certainly I will cast you away, says the Lord.’
“Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
34 And as for the prophet, and the priest, and the people who say, ‘The burden of the Lord!’ I will visit upon that man and upon his house.
In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
35 And then you will speak in this way, each one to his neighbor and to his brother: ‘What has the Lord answered? And what has the Lord said?’
Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
36 And the burden of the Lord will no longer be called to mind. For each one’s own word will be a burden. For you have perverted the words of the living God, of the Lord of hosts, our God.
Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
37 And then you will speak in this way to the prophet: ‘What has the Lord answered you? And what has the Lord spoken?’
Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
38 But if you say, ‘The burden of the Lord!’ then because of this, thus says the Lord: Since you have spoken this word, ‘The burden of the Lord!’ though I sent to you telling you not to say: ‘The burden of the Lord,’
Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
39 because of this, behold, I will take you away, like a burden, and I will forsake you, as well as the city that I gave to you and to your fathers, before my face.
Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
40 And I will give you over to an everlasting reproach and an eternal disgrace, which shall never be wiped away into oblivion.”
Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”

< Jeremiah 23 >