< Jeremiah 2 >

1 And the word of the Lord came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Go, and cry out to the ears of Jerusalem, saying: Thus says the Lord: I have remembered you, taking pity on your youth and on the charity of your betrothal, when you followed me into the desert, into a land which is not sown.
“Tafi ka yi shela a kunnuwar Urushalima cewa, “‘Na tuna da amincin ƙuruciyarki, yadda kamar amarya kika ƙaunace ni kika kuma bi ni cikin hamada, cikin ƙasar da ba a yi shuka ba.
3 Israel is holy to the Lord, the first of his fruits. All those who devour him commit an offense. Evils will overwhelm them, says the Lord.”
Isra’ila tsattsarka ce ga Ubangiji, nunan fari na girbinsa; dukan waɗanda suka cinye ta an same su da laifi, masifa kuwa ta same su,’” in ji Ubangiji.
4 Listen to the word of the Lord, O house of Jacob, and all you families of the house of Israel.
Ka saurari maganar Ubangiji, ya gidan Yaƙub, dukanku zuriyar gidan Isra’ila.
5 Thus says the Lord: “What iniquity have your fathers found in me, that they would draw far away from me, and would walk after emptiness, and would become empty?
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Wane laifi ne kakanninku sun same ni da shi, da suka tsaya nesa da ni? Sun bi gumakan banza su kansu suka kuma zama banza da kansu.
6 And they have not said: ‘Where is the Lord, who caused us to ascend from the land of Egypt; who led us through the desert, through an uninhabited and impassable land, through a land of drought and of the image of death, through a land in which no one walked and in which no man lived?’
Ba su yi tambaya, ‘Ina Ubangiji, wanda ya fitar da su daga Masar ya bishe su cikin jeji cikin hamada da kwazazzabai ƙasa mai fări da kuma duhu, ƙasar da ba kowa mai ratsa ta ba kowa kuma mai zama a cikinta?’
7 And I led you into the land of Carmel, so that you would eat from its fruit and from its excellence. And having entered it, you defiled my land, and you turned my inheritance into an abomination.
Na kawo ku zuwa ƙasa mai albarka don ku ci amfaninta da abubuwa masu yalwar da take bayarwa. Amma kuka zo kuka ƙazantar da ƙasata kuka kuma mai da gādona abin ƙyama.
8 The priests have not said: ‘Where is the Lord?’ And those who held the law did not know me. And the pastors betrayed me. And the prophets prophesied in Baal and followed idols.
Firistoci ba su yi tambaya, ‘Ina Ubangiji ba.’ Waɗanda suke amfani da doka ba su san ni ba; shugabanni suka yi mini tawaye. Annabawa suka yi annabci ta wurin Ba’al, suna bin gumakan banza.
9 Because of this, I will still contend in judgment against you, says the Lord, and I will dispute with your sons.
“Saboda haka ina sāke tuhumarku,” in ji Ubangiji. “Zan kuma tuhumi’ya’ya’ya’yanku.
10 Cross over to the isles of Kittim, and gaze. And send to Kedar, and consider diligently. And see if anything like this has ever been done.
Ku ƙetare zuwa tsibiran Kittim ku gani, ku aika zuwa Kedar ku duba da kyau; ku ga ko an taɓa yin wani abu haka.
11 See if a nation has ever changed their gods, though certainly those are not gods. Yet truly, my people have exchanged their glory for an idol.
Akwai wata al’ummar da ta canja allolinta? (Duk da haka su ba alloli ba ne sam.) Amma mutanena sun musayar da ɗaukakarsu da gumakan banza.
12 Be astonished at this, O heavens, and be utterly desolate, O gates of heaven, says the Lord.
Ku girgiza saboda wannan, ya sammai, ku kuma razana don tsoro mai girma,” in ji Ubangiji.
13 For my people have done two evils. They have forsaken me, the Fountain of living water, and they have dug for themselves cisterns, broken cisterns that are unable to hold water.
“Mutanena sun aikata zunubai guda biyu. Sun rabu da ni, ni da nake maɓulɓular ruwan rai, sun kuma haƙa tankunan ruwansu, tankuna ruwan da suka fashe da ba za su iya riƙe ruwa ba.
14 Is Israel a servant, or one born into slavery? Then why has he become a prey?
Isra’ila bawa ne, bawa ne ta wurin haihuwa? Me ya sa ya zama ganima?
15 The lions have roared over him, and they have uttered their voice. They have set his land in solitude; his cities have been burned up, and there is no one who lives in them.
Zakoki sun yi ruri; sun yi masa ruri. Sun lalatar da ƙasarsa; an ƙone garuruwansa aka kuma watse daga ciki.
16 Likewise, the sons of Memphis and of Tahpanhes have defiled you, even to the top of the head.
Haka ma, mutanen Memfis da Tafanes sun aske rawanin kanka
17 Has this not been done to you because you abandoned the Lord your God, in that time when he was leading you by the way?
Ba kai ne ba ka jawo wa kanka ba ta wurin rabuwa da Ubangiji Allahnka sa’ad da ya bi da kai a hanya?
18 And now what do you want from the way of Egypt, but to drink their turbid water? And what do you want from the way of the Assyrians, but to drink the water of their river?
To, me ya sa za ka Masar don shan ruwa daga Shihor? Kuma me ya sa za ka Assuriya don shan ruwa daga Kogi?
19 Your own malice will reprove you, and your own apostasy will rebuke you! But know and perceive this: it is an evil and bitter thing for you to forsake the Lord your God, and to be without my fear within you, says the Lord, the God of hosts.
Muguntarka za tă hukunta ka; jan bayanka zai tsawata maka. Sai ka lura ka kuma gane yaya mugu da kuma ɗaci suke a gare ka sa’ad da ka rabu da Ubangiji Allahnka kuma ba ka tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
20 From ancient times, you have broken my yoke; you have torn apart my bonds, and you have said, ‘I will not serve.’ For on every high hill, and under every leafy tree, you have been debased, O harlot.
“Tun da daɗewa ka karya karkiyarka ka kuma tsintsinke sarƙoƙinka; sai ka ce, ‘Ba zan bauta maka ba!’ Tabbatacce, a kan kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane ɗanyen itace ka kwanta kamar karuwa.
21 Yet I planted you as an elect vineyard, with only true seed. Then how have you been turned away from me, toward that which is depraved, O strange vineyard?
Na shuka ka kamar zaɓaɓɓen inabi iri mai kyau da kuma wanda za a dogara a kai. Yaya kuma ka juya kana gāba da ni ka lalace, ka zama inabin jeji?
22 Even if you wash yourself with soap, and increase your use of herbal soaps, you are still stained by your iniquity in my sight, says the Lord God.
Ko da yake ka wanke kanka da sabulu ka yi amfani da sabulu mai yawa, duk da haka har yanzu tabon laifinka yana nan a gabana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
23 How can you say: ‘I have not been polluted. I have not walked after Baal?’ Consider your ways in the steep valley. Acknowledge what you have done, so that you may be like a swift runner, following his course.
“Yaya za ka ce, ‘Ban ƙazantu ba; ban bi Ba’al ba’? Duba yadda ka yi a cikin kwari; ka ga abin da ka yi. Kai kamar makwaɗaciyar raƙuma ce mai zafin gudu kana gudu nan da can,
24 A wild donkey accustomed to solitude, out of the desire in his soul, caught the scent of his lover. Now nothing will turn him away from her. All those who seek her will not cease. But they will find her in her menstruation.
kamar jakar jejin da ta saba da hamada, mai busar iska cikin son barbaranta sa’ad da take son barbara wa zai iya hana ta? Jakin da yake nemanta, ba ya bukatar wahalar da kansa; a lokacin barbara za a same ta.
25 You should keep your foot from being naked, and your throat from being thirsty. But you have said: ‘I have lost hope. I will not do it. For certainly, I have loved strangers, and I will walk after them.’
Kada ka yi gudu har ƙafafunka su zama ba takalma maƙogwaronka kuma ya bushe. Amma sai ka ce, ‘Ba amfani! Ina ƙaunar baƙin alloli kuma dole in bi su.’
26 In the same way that a thief is confounded when he has been apprehended, so the house of Israel has been confounded, they and their kings, their leaders and priests and prophets.
“Kamar yadda akan kunyatar da ɓarawo sa’ad da aka kama shi, haka gidan Isra’ila zai sha kunya, su, sarakunansu da shugabanninsu, firistocinsu da kuma annabawansu.
27 For they say to a piece of wood, ‘You are my father,’ and to a stone, ‘You have conceived me.’ They have turned their back to me, and not their face. But in the time of their affliction, they will say: ‘Rise up and deliver us.’
Kuna ce wa itace, ‘Kai ne mahaifina,’ ga dutse kuma, ‘Kai ne ka haife ni.’ Sun juye mini bayansu ba fuskokinsu ba; duk da haka sa’ad da suna cikin wahala, sukan ce, ‘Zo ka cece mu!’
28 Where are your gods that you made for yourselves? Let them rise up and deliver you in the time of your affliction. For certainly, your gods were like the number of your cities, O Judah.
To ina allolin da kuka yi wa kanku? Bari su zo in suna iya cetonku sa’ad da kuke cikin wahala! Gama kuna da alloli masu yawa kamar yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda.
29 Why do you want to contend against me in judgment? You have all forsaken me, says the Lord.
“Me ya sa kuke tuhumana? Dukanku kun yi mini tawaye,” in ji Ubangiji.
30 I have struck your children to no effect; they have not accepted discipline. Your own sword has devoured your prophets. Your generation is like a raging lion.
“A banza na hukunta mutanenku; ba su yi gyara ba. Takobinku ya cinye annabawanku kamar zaki mai jin yunwa.
31 Consider the word of the Lord. Have I become like a wilderness to Israel, or like a land late to bear fruit? Then why have my people said, ‘We are withdrawing; we will no longer approach you’?
“Ku na wannan zamani, ku saurari maganar Ubangiji. “Na zama wa Isra’ila hamada ne ko ƙasa mai babban duhu? Me ya sa mutanena suke cewa, ‘Muna da’yanci mu yi ta yawo; ba za mu ƙara zuwa wurinka ba’?
32 Can a virgin forget her ornament, or a bride the covering across her breast? Yet truly, my people have forgotten me, for innumerable days.
Budurwa za tă manta da kayan adonta amarya ta manta da kayan adon aurenta? Duk da haka mutanena sun manta da ni, kwanaki ba iyaka.
33 Why are you striving to claim that your way is good, as if to seek my love, when all the while you are also displaying your malice by your own way,
Kuna da azanci sosai a bin masoya! Kai, ko mafiya muni cikin mata tana iya koya daga hanyoyinku.
34 and in your armpits there is found the blood of poor and innocent souls? I have found them, not in ditches, but everywhere that I mentioned previously.
A rigunanku mutane kan sami jinin matalauta marasa laifi, ko da yake ba ku kama su suna fasawa su shiga ba. Duk da haka
35 And you have said: ‘I am innocent and without sin. And because of this, let your fury be turned away from me.’ Behold, I will contend with you in judgment, because you have said: ‘I have not sinned.’
kuna cewa, ‘Ba ni da laifi; ba ya fushi da ni.’ Amma zan zartar da hukunci a kanku domin kun ce, ‘Ban yi zunubi ba.’
36 How exceedingly vile you have become, repeating your ways again and again! And so, you will be ashamed of Egypt, just as you were ashamed of Assur.
Don me kuke yawo da yawa haka, kuna ta canjin hanyoyinku? Masar za tă kunyata ku yadda kuka sha kunya a wurin Assuriya.
37 For you will also depart from that place, and your hand will be upon your head. For the Lord has crushed your confidence, and you will have nothing prosperous by it.”
Za ku kuma bar wurin da hannuwanku a kanku, gama Ubangiji ya ƙi waɗanda kuka amince da su; ba za ku zama abin taimako a gare su ba.

< Jeremiah 2 >