< Jeremiah 12 >

1 Certainly, O Lord, you are just. But if I may contend with you, while still speaking what is just to you: Why does the way of the impious prosper? Why is it well with all those who transgress and act unfairly?
Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
2 You planted them, and they took root. They are prospering and bearing fruit. You are near to their mouths, but far from their hearts.
Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
3 And you, O Lord, have known me well. You have seen me, and you have tested my heart with you. Gather them together like a flock for the sacrifice and sanctify them for the day of slaughter.
Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
4 How long shall the earth mourn? And how long shall the plants of every field whither because of the wickedness of the inhabitants within them? It has consumed the wild animals and the birds. For they said: “He will not see our very end.”
Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
5 “If you have struggled to run on foot, how will you be able to compete with horses? And if you have been secure in a land of peace, what will you do about the arrogance of the Jordan?
“In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
6 For even your brothers, and the house of your father, even these have fought against you. And they have cried out after you with loud voice: ‘You should not believe them, when they speak good things to you.’”
’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
7 “I have abandoned my house. I have disowned my inheritance. I have given my beloved soul into the hand of its enemies.
“Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
8 My inheritance has become for me like a lion in the forest. It has uttered a voice against me, therefore, I have hated it.
Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
9 Is my inheritance to me like a discolored bird? Is it like a bird that has entirely changed color? Approach and assemble, all beasts of the earth! Hurry, so that you may devour!
Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
10 Many pastors have demolished my vineyard. They have trampled my portion. They have made my desirable portion into a desert of solitude.
Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
11 They have squandered it, and it has grieved concerning me. The entire earth has become utterly desolate, because there is no one who understands with the heart.”
Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
12 The devastators have arrived, over all the ways of the wilderness. For the sword of the Lord will devour, from one end of the earth even to its furthest limits. There is no peace for all that is flesh.
A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
13 They sowed wheat, but they reaped thorns. They received an inheritance, but it will not benefit them. You will be confounded by your own fruits, because of the wrath of the fury of the Lord.
Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
14 Thus says the Lord against all my wicked neighbors, who touch the inheritance that I have distributed to my people Israel: “Behold, I will root them out of their own land, and I will root the house of Judah out of their midst.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
15 And when I have rooted them out, I will turn back and take pity on them. And I will lead them back, one man to his inheritance, and another man to his land.
Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
16 And this shall be: if they are taught and they learn the ways of my people, so that they swear by my name, ‘As the Lord lives,’ just as they had taught my people to swear by Baal, then they will be built up in the midst of my people.
In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
17 But if they will not listen, I will uproot that nation unto utter destruction and perdition, says the Lord.”
Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.

< Jeremiah 12 >