< Isaiah 46 >

1 Bel has been broken. Nebo has been crushed. Their idols have been placed upon beasts and cattle, your grievous heavy burdens, even unto exhaustion.
Bel ya rusuna, Nebo ya durƙusa ƙasa; ana ɗaukan gumakansu a kan dabbobi ne. Siffofin da ake yawo da su nawaya ne, kayan nauyi masu gajiyarwa.
2 They have been melted down, or have been smashed together. They were not able to save the one who carried them, and their life will go into captivity.
Sun durƙusa suka kuma rusuna tare; ba su iya kuɓutar da nauyin kaya su kansu sukan tafi bauta.
3 Listen to me, house of Jacob, all the remnant of the house of Israel, who are carried in my bosom, who were born from my womb.
“Ku kasa kunne gare ni, ya ku gidan Yaƙub, dukanku waɗanda kuka rage na gidan Isra’ila, ku da na lura da ku tun da aka yi cikinku, na kuma riƙe ku tun haihuwarku.
4 Even to your old age, I am the same. And even with your grey hairs, I will carry you. I have made you, and I will sustain you. I will carry you, and I will save you.
Har lokacin da kuka tsufa kuka yi furfura ni ne shi, ni ne shi wanda zai lura da ku. Na yi ku zan kuma riƙe ku; zan lura da ku in kuma kuɓutar da ku.
5 To whom would you liken me, or equate me, or compare me, or consider me to be similar?
“Da wa za ku kwatanta ni ko ku ɗauka daidai da ni? Da wa nake kama da har da za ku kwatanta ni?
6 You take gold from a bag, and you weigh silver on a scale, so as to hire a goldsmith to make a god. And they fall prostrate and adore.
Waɗansu sukan zubar da zinariya daga jaka su kuma auna azurfa a ma’auni; sukan yi haya maƙerin zinariya don yă ƙera allah, su kuma rusuna su yi masa sujada.
7 They carry him on their shoulders, supporting him, and they set him in his place. And he will stand still and will not move from his place. But even when they will cry out to him, he will not hear. He will not save them from tribulation.
Sukan daga shi a kafaɗunsu su kuma ɗauke shi; sukan kafa shi a tsaye a wurinsa, a can kuwa zai tsaya. Daga wannan wuri ba zai iya gusawa ba. Ko da wani ya nemi taimakonsa, ba ya amsawa; ba zai iya cetonsa daga wahala ba.
8 Remember this, and be confounded. Return, you transgressors, to the heart.
“Ku tuna da wannan, ku sa shi a zuciya, ku riƙe shi a zuciya, ku’yan tawaye.
9 Remember the past ages. For I am God, and there is no other god. There is no one like me.
Ku tuna da abubuwan da suka riga suka faru, waɗannan na tun dā; ni ne Allah, kuma babu wani; ni ne Allah kuma babu wani kamar ni.
10 From the beginning, I announce the last things, and from the start, the things that have not yet been done, saying: My plan will stand firm, and my entire will shall be done.
Nakan sanar da ƙarshe tun daga farko, daga fil azal, abin da yake zuwa nan gaba. Na ce nufina zai tabbata, kuma zan aikata dukan abin da na gan dama.
11 I call a bird from the east, and from a far away land, the man of my will. And I have spoken it, and I will carry it out. I have created, and I will act.
Daga gabas na kira tsuntsun da yake farauta; daga can ƙasa mai nesa, wani mutumin da zai cika nufina. Abin da na riga na faɗa, shi zan sa ya faru; abin da na shirya, shi zan aikata.
12 Hear me, you who are hard of heart, who are far from justice!
Ku kasa kunne, ku masu taurinkai, ku da kuke nesa da adalci.
13 I have brought my justice near. It will not be far away, and my salvation will not be delayed. I will grant salvation in Zion, and my glory in Israel.
Ina kawo adalcina kusa, ba shi da nisa; kuma cetona ba zai jinkirta ba. Zan yi wa Sihiyona ceto, darajata ga Isra’ila.

< Isaiah 46 >