< Isaiah 25 >

1 O Lord, you are my God! I will exalt you, and I will confess your name. For you have accomplished miracles. Your plan, from antiquity, is faithful. Amen.
Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
2 For you have appointed a city as a tomb, a strong city for ruination, a house of foreigners: so that it may not be a city, and so that it may not be rebuilt forever.
Ka mai da birnin tsibin tarkace, ka lalatar da gari mai katanga, birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.
3 Concerning this, a strong people will praise you; a city with a robust people will fear you.
Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka; biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.
4 For you have been the strength of the poor, the strength of the indigent in his tribulation, a refuge from the whirlwind, a shadow from the heat. For the spirit of the mighty is like a whirlwind striking against a wall.
Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa, wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana. Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango
5 You will bring low the uprising of foreigners, just as heat brings thirst. And like heat under a torrential cloud, you will cause the offshoot of the strong to wither away.
kuma kamar zafin hamada. Ka kwantar da hayaniyar baƙi; kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.
6 And the Lord of hosts will cause all the peoples on this mountain to feast on fatness, to feast on wine, a fatness full of marrow, a purified wine.
A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane, liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.
7 And he will cast down violently, on this mountain, the face of the chains, with which all peoples had been bound, and the net, with which all nations had been covered.
A wannan dutse zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane, ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;
8 He will violently cast down death forever. And the Lord God will take away the tears from every face, and he will take away the disgrace of his people from the entire earth. For the Lord has spoken it.
zai haɗiye mutuwa har abada. Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye daga dukan fuskoki; zai kawar da kunyar mutanensa daga dukan duniya. Ubangiji ne ya faɗa.
9 And they will say in that day: “Behold, this is our God! We have waited for him, and he will save us. This is the Lord! We have endured for him. We will exult and rejoice in his salvation.”
A wannan rana za su ce, “Tabbatacce wannan shi ne Allah; mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu. Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi; bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa.”
10 For the hand of the Lord will rest upon this mountain. And Moab will be trampled under him, just as stubble is worn away by a wagon.
Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse; amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.
11 And he will extend his hands under him, like a swimmer extending his hands to swim. And he will bring down his glory with a clap of his hands.
Za su buɗe hannuwansa a cikinsa, yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo. Allah ya ƙasƙantar da girmankansu duk da wayon hannuwansu.
12 And the fortifications of your sublime walls will fall, and be brought low, and be torn down to the ground, even to the dust.
Zai rurrushe manyan katangar kagaru ya kuma ƙasƙantar da su; zai rushe su har ƙasa, su zama ƙura.

< Isaiah 25 >