< Isaiah 23 >

1 The burden of Tyre. Wail, you ships of the sea! For the house, from which they were accustomed to go forth, has been laid waste. From the land of Kittim, this has been revealed to them.
Abin da Allah ya faɗa game da Taya. Ku yi kuka mai zafi, ya jiragen ruwan Tarshish! Gama an hallaka Taya aka kuma bar su babu gida ko tasha. Daga ƙasar Saifurus magana ta zo musu.
2 Be silent, you inhabitants of the island! The merchants of Sidon, crossing over the sea, have filled you.
Ku yi shiru, ku mutanen tsibiri da ku’yan kasuwan Sidon waɗanda masu ciniki a teku suka azurta.
3 The offspring of the Nile is in the midst of many waters. The harvest of the river is her crop. And she has become the marketplace of the nations.
A manyan ruwaye hatsin Shihor suka iso; girbin Nilu ne kuɗin shiga na Taya ta kuma zama kasuwar al’ummai.
4 Be ashamed, O Sidon! For the sea speaks, the strength of the sea, saying: “I have not been in labor, and I have not given birth, and I have not raised young men, nor have I promoted the development of virgins.”
Ki ji kunya, ya ke Sidon, da ke kuma, kagarar teku, gama teku ya yi magana ya ce, “Ban taɓa naƙuda ba balle in haifi’ya’ya; ban taɓa goyon’ya’ya maza ba balle in reno’ya’ya mata.”
5 When it has been heard in Egypt, they will be in anguish, when they hear of Tyre.
Sa’ad da magana ta kai Masar, za su razana da jin labari daga Taya.
6 Cross over the seas. Wail, you inhabitants of the island!
Ku haye zuwa Tarshish; ku yi kuka mai zafi, ku mutanen tsibiri.
7 Is this not your place, which from its earliest days has gloried in its antiquity? Her feet will lead her to a sojourn far away.
Wannan ce birnin murnanku, birnin nan na tun dā wadda ƙafafunta suka kai ta zama a ƙasashe masu nesa?
8 Who has made this plan against Tyre, which formerly was crowned, whose merchants were leaders, whose traders were illustrious on the earth?
Wane ne ya ƙulla wannan a kan Taya ita da take ba da rawanin sarauta, wadda’yan kasuwanta sarakuna ne, wadda masu cinikinta sanannu ne a duniya?
9 The Lord of hosts has planned this, so that he may tear down the arrogance of all glory, and may bring disgrace to all the illustrious of the earth.
Ubangiji Maɗaukaki ya ƙulla shi, don yă kawo ƙarshen girman kan dukan darajarta ya kuma ƙasƙantar da dukan waɗanda suke sanannu a duniya.
10 Cross through your land, as through a river, O daughter of the sea. You no longer have a belt.
Ki nome ƙasarki har zuwa wajen Nilu, Ya Diyar Tarshish, gama ba ki da tashan jirgin ruwa kuma.
11 He has extended his hand over the sea. He has stirred up kingdoms. The Lord has given an order against Canaan, so that he may crush its strong.
Ubangiji ya miƙa hannunsa a bisa teku ya kuma sa mulkokinsa suka yi rawar jiki. Ya ba da umarni game da Funisiya cewa a hallaka kagararta.
12 And he said: “You shall no longer increase so as to glory, while enduring calumny, O virgin daughter of Sidon. Rise up and set sail for Kittim; in that place, too, there will be no rest for you.”
Ya ce, “Ba za ki ƙara yin murna ba, Ya ke Budurwa Diyar Sidon, yanzu da kike ragargajiya! “Tashi, ki ƙetare zuwa Saifurus; a can ɗin ma ba za ki huta ba.”
13 Behold, the land of the Chaldeans: never before was there such a people! Assur founded it. They have led away its strong ones into captivity. They have dug under its houses. They have left it in ruins.
Dubi ƙasar Babiloniyawa, wannan mutanen da yanzu ba su da wani amfani! Assuriyawa sun mai da ita wurin zaman halittun hamada; sun gina hasumiyoyin kwanto, suka ragargaza kagararta ƙaf suka mai da ita kango.
14 Wail, you ships of the sea! For your strength has been devastated.
Ku yi kuka mai zafi, ku jiragen ruwan Tarshish; an rurrushe kagararku!
15 And this shall be in that day: you, O Tyre, will be forgotten for seventy years, like the days of one king. Then, after seventy years, there will be, for Tyre, something like the canticle of a harlot.
A wannan lokaci za a manta da Taya har shekaru saba’in, tsawon rayuwar sarki. Amma a ƙarshen waɗannan shekaru saba’in, zai zama wa Taya kamar yadda yake a waƙar karuwa cewa,
16 Take up a stringed instrument. Circulate through the city, you harlot who had been forgotten. Sing many canticles well, so that you may be remembered.
“Ɗauki garaya, ki ratsa birni, Ya ke karuwar da aka manta da ita; kaɗa garaya da kyau, ki rera waƙoƙi masu yawa, saboda a tuna da ke.”
17 And this shall be after seventy years: the Lord will visit Tyre, and he will lead her back to her profits. And she will fornicate again with all the kingdoms of the world upon the face of the earth.
A ƙarshen shekaru saba’in, Ubangiji zai magance Taya. Za tă koma ga aikinta na karuwanci za tă kuma yi kasuwancinta da dukan mulkokin duniya.
18 And her businesses and her profits will be sanctified to the Lord. They will not be locked away and they will not be stored. For her business will be for those who will live in the presence of the Lord, so that they may eat until satisfied, and may be well-clothed even into old age.
Duk da haka za a keɓe ribarta da kuɗin shigarta wa Ubangiji; ba za a yi ajiyarsu ko a ɓoye su. Ribarta za tă tafi ga waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada, don su sami yalwataccen abinci da tufafi masu kyau.

< Isaiah 23 >