< Hosea 4 >

1 Listen to the word of the Lord, sons of Israel, for the Lord is judge of the inhabitants of the land. Yet there is no truth, and there is no mercy, and there is no knowledge of God, in the land.
Ku ji maganar Ubangiji, ku Isra’ilawa, gama Ubangiji yana da tuhumar da zai kawo a kan ku waɗanda suke zama a ƙasar. “Babu aminci, babu ƙauna, babu yarda da Allah a cikin ƙasar.
2 Slander, and lying, and killing, and theft, and adultery have overflowed, and bloodshed has brought more bloodshed.
Akwai la’ana ce kawai, yin ƙarya da kisa, yin sata da zina; sun wuce gona da iri, kisankai a kan kisankai.
3 Because of this, the land will mourn, and all who dwell in it will languish, with the beasts of the field and the birds of the air. And the fishes of the sea also will be gathered together.
Saboda wannan ƙasar tana makoki, kuma dukan waɗanda suke zama a cikinta sun lalace; namun jeji da tsuntsayen sararin sama da kuma kifin teku suna mutuwa.
4 So, truly, let each and every one not judge, and let no man be accused, for your people are just like those who speak against the priesthood.
“Amma kada wani mutum yă kawo tuhuma, kada wani mutum yă zargi wani, gama mutanenka suna kama da waɗanda suke kawo tuhume-tuhume a kan firist ne.
5 And you will be ruined on this day, and now the prophet will be ruined with you. In the night, I have made your mother to be silent.
Kuna tuntuɓe dare da rana, annabawa ma suna tuntuɓe tare da ku. Saboda haka zan hallaka mahaifiyarku,
6 My people have become silent because they had no knowledge. Since you have rejected knowledge, I will drive you away; you do not perform the duties of the priesthood for me, and you have forgotten the law of your God, and so I will forget your sons.
mutanena suna hallaka saboda jahilci. “Domin kun ƙi neman sani, ni ma na ƙi ku a matsayin firistocina; domin kun ƙyale dokar Allahnku, ni ma zan ƙyale’ya’yanku.
7 According to the multitude of them, so have they sinned against me. I will change their glory into disgrace.
Yawan ƙaruwar firistoci, haka suke yawan zunubi a kaina; sun yi musaya Ɗaukakarsu da wani abin kunya.
8 They will devour the sins of my people, and they will lift up their souls towards their iniquity.
Suna ciyar da kansu a kan zunuban mutanena suna kuma haɗamar muguntarsu.
9 And, just as it is with the people, so will it be with the priest; and I will visit their ways upon them, and I will repay them for their intentions.
Zai kuwa zama, kamar yadda mutane suke, haka firistoci suke. Zan hukunta dukansu saboda al’amuransu in kuma sāka musu saboda ayyukansu.
10 And they will eat and not be satisfied. They have been committing fornication, and they did not cease. Since they have abandoned the Lord, they will not be safeguarded.
“Za su ci amma ba za su ƙoshi ba; za su shiga karuwanci amma ba za su ƙaru ba, gama sun rabu da Ubangiji don su ba da kansu
11 Fornication, and wine, and drunkenness, have taken away their heart.
ga karuwanci, ga tsoho da kuma sabon ruwan inabi, waɗanda suka ɗauke ganewar mutanena.
12 My people have inquired of their stave, and their staff has announced to them. For the spirit of fornication has deceived them, and they have been fornicating before their God.
Sun nemi shawarar gunkin da aka yi da itace suka kuwa sami amsa daga sanda. Halin karuwanci yakan ɓad da su; sun yi rashin aminci ga Allahnsu.
13 They have offered sacrifice on the tops of the mountains and burnt incense on the hills, under the oak, and the poplar, and the terebinth tree, because its shadow was good; therefore, your daughters will commit fornication and your spouses will be adulteresses.
Suna miƙa hadaya a kan ƙwanƙolin duwatsu suna kuma ƙone hadayu a kan tuddai, a ƙarƙashin itatuwa oak, aduruku da katambiri, inda inuwa take da daɗi. Saboda haka’ya’yanku mata suka juya wa karuwanci surukanku mata kuma suka shiga yin zina.
14 I will not send afflictions on your daughters, when they will commit fornication, nor on your spouses, when they will commit adultery, because you yourselves have associated with harlots and have offered sacrifice with the effeminate, and because the people who do not understand will be defeated.
“Ba zan hukunta’ya’yanku mata sa’ad da suka juya ga yin karuwanci ba, balle surukanku mata, sa’ad da suka yi zina, gama mazan da kansu suna ma’amala da karuwai suna kuma miƙa hadaya tare da karuwai na masujada, mutane marasa ganewa za su lalace!
15 If you commit fornication, Israel, at least let Judah not commit offenses; and do not be willing to enter into Gilgal, nor to ascend to Bethaven, and neither should you swear, “As the Lord lives.”
“Ko da yake kun yi zina, ya Isra’ila, kada Yahuda ya yi laifi. “Kada ku tafi Gilgal; kada ku haura zuwa Bet-Awen. Kuma kada ku rantse cewa, ‘Muddin Ubangiji yana a raye!’
16 For Israel has gone astray like a wanton heifer; so now the Lord will pasture them like a young lamb in a wide expanse.
Isra’ilawa masu taurinkai ne, kamar karsana mai taurinkai. Yaya Ubangiji zai iya kiwonsu kamar tumaki a makiyaya mai ɗanyar ciyawa?
17 Ephraim participates in idolatry, so send him away.
Efraim ya haɗa kai da gumaka; ku ƙyale shi kurum!
18 Their feasting has been set aside; they have committed fornication after fornication. They love to bring disgrace to their protectors.
Ko ma sa’ad da abin shansu ya ƙare, sai suka ci gaba da karuwancinsu; masu mulkinsu suna ƙaunar abin kunya.
19 The wind has fastened them to its wings, and they will be confounded because of their sacrifices.
Guguwa za tă share su, hadayunsu kuma za su jawo musu abin kunya.

< Hosea 4 >