< Hosea 2 >

1 “Say to your brothers, ‘You are my people,’ and to your sister, ‘You have obtained mercy.’
“Ka ce da’yan’uwanka maza, ‘Mutanena,’ ka kuma ce da’yan’uwanka mata, ‘Ƙaunatacciyata.’
2 Judge your mother, judge: for she is not my wife, and I am not her husband. Let her remove her fornications from before her face and her adulteries from between her breasts.
“Ka tsawata wa mahaifiyarka, ka tsawata mata, gama ita ba matata ba ce, ni kuma ba mijinta ba ne. Ku roƙe ta tă daina karuwancinta da kuma rashin aminci a tsakanin nononta.
3 Otherwise, I may expose her nakedness and set her as on the day of her birth, and I may establish her as a wilderness and set her as an impassable land, and I may execute her with thirst.
In ba haka ba zai tuɓe ta tsirara in bar ta kamar yadda take a ranar da aka haife ta; zan sa ta zama kamar hamada, in mayar da ita busasshiyar ƙasar, in kashe ta da ƙishirwa.
4 And I will not have mercy on her sons, for they are the sons of fornications.
Ba zan nuna wa’ya’yanta ƙaunata ba, domin su’ya’yan zina ne.
5 For their mother has been fornicating; she who conceived them has been brought to ruin. For she said, ‘I will go after my lovers, who give me my bread and my water, my wool and my flax, my oil and my drink.’
Mahaifiyarsu ta yi rashin aminci ta kuma ɗauki cikinsu ta wurin yi abin kunya. Ta ce, ‘Zan bi kwartayena, waɗanda suke ba ni abinci da ruwa, ulu nawa da lilina, mai nawa da kuma abin sha na.’
6 Because of this, behold, I will fence in your way with thorns, and I will surround it with a wall, and she will not find her paths.
Saboda haka zai tare hanyarta da ƙaya; zan yi mata katanga don kada tă sami hanya.
7 And she will pursue her lovers, but she will not obtain them, and she will seek them, but she will not find them, and she will say, ‘I will go and return to my first husband, because it was to some extent better for me then, than it is now.’
Za tă bi kwartayenta amma ba za tă kama su ba; za tă neme su amma ba za tă same su ba. Sa’an nan za tă ce, ‘Zan koma ga mijina na fari, gama dā ya fi mini yadda nake a yanzu.’
8 And she did not know that I gave her grain and wine and oil, and that I increased her silver and gold, which they made into Baal.
Ba ta yarda cewa ni ne wanda ya ba ta hatsi, sabon ruwan inabi da mai ba, wanda ya jibge mata azurfa da zinariya, waɗanda suka yi amfani wa Ba’al ba.
9 For this reason, I will turn back, and I will take away my grain in its time and my wine in its time, and I will set free my wool and my flax, which had covered her disgrace.
“Saboda haka zan ƙwace hatsina sa’ad da ya nuna, da sabon ruwan inabina sa’ad da ya ƙosa. Zan karɓe ulu nawa da lilina, da take niyya ta rufe tsiraicinta.
10 And now, I will reveal her foolishness by the eyes of her lovers, and no man will rescue her from my hand.
Saboda haka yanzu zan buɗe tsiraicinta a idanun kwartayenta; ba wani da zai ƙwace ta daga hannuwana.
11 And I will cause all her joy to cease: her solemnities, her new moons, her Sabbaths, and all her feast dates.
Zan tsayar da dukan bukukkuwarta, bukukkuwarta na shekara-shekara, da kuma kiyaye bikin Sababbin Wata nata, kwanakin Asabbacinta, dukan ƙayyadaddun bukukkuwarta.
12 And I will corrupt her vines and her fig trees, about which she said, ‘These rewards, they are mine, my lovers have given them to me.’ And I will place her in a narrow forest, and the beasts of the field will devour her.
Zan lalatar da inabinta da kuma itatuwan ɓaurenta, waɗanda take cewa su ne abin da kwartayenta suka biya; zan mayar da su kurmi, namun jeji kuwa za su ci su.
13 And I will inflict on her the days of the Baals, for whom she burned incense, and ornamented herself with earrings and necklace, and went after her lovers, and forgot about me,” says the Lord.
Zan hukunta ta saboda kwanakin da ta ƙone turare wa Ba’al; ta yi wa kanta ado da zobai da duwatsu masu daraja, ta bi kwartayenta, amma ta manta da ni,” in ji Ubangiji.
14 “Because of this, behold, I will attract her, and I will lead her into the wilderness, and I will speak to her heart.
“Saboda haka yanzu zan rarrashe ta; zan bishe ta zuwa hamada in kuma yi mata magana a hankali.
15 And I will give to her, from the same place, her vinedressers, and the valley of Achor as a passage of hope. And she will sing there as in the days of her youth, and as in the days of her ascension from the land of Egypt.
A can zan mayar mata da gonakin inabinta, zan kuma sa Kwarin Akor yă zama ƙofar bege. A can za tă rera kamar a kwanakin ƙuruciyarta, kamar a lokacin da ta fita daga Masar.
16 And it will be in that day,” says the Lord, “that she will call me, ‘My Husband,’ and she will no longer call me, ‘My Baal.’
“A waccan rana,” in ji Ubangiji, “za ki ce da ni ‘mijina’; ba za ki ƙara ce ni ‘maigidana’ ba.
17 And I will remove the names of the Baals from her mouth, and she will no longer remember their name.
Zan cire sunayen Ba’al daga leɓunanta; ba za a ƙara kira sunayensu ba.
18 And in that day, I will strike a deal with them, with the beasts of the field, and with the birds of the sky, and with the creatures of the earth. And I will crush the bow and the sword, and I will wipe away war from the earth. And I will let them sleep securely.
A waccan rana zan yi alkawari dominsu da namun jeji da kuma tsuntsayen sararin sama da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa. Baka da takobi da yaƙi zan sa su ƙare a ƙasar, domin duk su zauna lafiya.
19 And I will betroth you to me forever, and I will betroth you to me in justice and judgment, and in mercy and compassion.
Zan ɗaura aure da ke har abada; zan ɗaura aure da yake cikin adalci da gaskiya, cikin ƙauna da jinƙai.
20 And I will wed you to me in faith, and you will know that I am the Lord.
Zan ɗaura aure da yake cikin aminci za ki kuwa yarda cewa ni ne Ubangiji.
21 And this will happen in that day: I will listen closely,” says the Lord. “I will hear the heavens, and they will hear the earth.
“A waccan rana zan amsa,” in ji Ubangiji, “zan amsa wa sararin sama, za su kuwa amsa wa ƙasa;
22 And the land will pay attention to the grain, and the wine, and the oil; and these will hear Jezreel.
ƙasa kuma za tă amsa wa hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai, su kuma za su amsa wa Yezireyel.
23 And I will plant her for me in the land, and I will have mercy on her, though she had been called Without Mercy. And I will say to Not My People, ‘You are my people,’ and they will say, ‘You are my God.’”
Zan dasa ta wa kaina a ƙasar; zan shuka ƙaunata ga wanda na ce ‘Ba ƙaunatacciyata ba.’ Zan faɗa wa waɗanda a ce ‘Ba mutanena ba,’ ‘Ku mutanena ne’; za su kuwa ce, ‘Kai ne Allahna.’”

< Hosea 2 >