< Daniel 12 >

1 “But at that time Michael will rise up, the great leader, who stands up for the sons of your people. And a time will come, such as has not been from the time that nations began, even until that time. And, at that time, your people will be saved, all who will be found written in the book.
“A wannan lokaci Mika’ilu, babban mai mulki wanda yake kāre mutanenka, zai tashi. Za a yi lokacin matsananciyar wahala wanda ba a taɓa yi tun farkon ƙasashe har zuwa yanzu. Amma a lokacin da mutanenka, kowane mutum wanda aka sami sunansa a rubuce a cikin littafin, za a cece shi.
2 And many of those who sleep in the dust of the earth will awaken: some to everlasting life, and others to a reproach that they will always see.
Ɗumbun mutanen da suka yi barci cikin turɓayar duniya za su farka, waɗansu zuwa ga rai madawwami, waɗansu zuwa ga madawwamiyar kunya da kuma madawwamin ƙasƙanci.
3 But those who have taught will shine like the brightness of the firmament, and those who instruct many towards justice, like the stars for unending eternity.
Waɗanda suke da hikima za su haskaka kamar hasken samaniya, waɗanda kuma suka jagoranci waɗansu da yawa zuwa adalci, za su zama kamar taurari har abada abadin.
4 But you, Daniel, close the message and seal the book, until the established time. Many will pass through, and knowledge will be increased.”
Amma kai, Daniyel, ka rufe zancen nan ka kuma liƙe kalmomin littafin nan har sai ƙarshe. Mutane da yawa za su yi ta kai komo don neman sani.”
5 And I, Daniel, looked, and behold, similarly two others stood up, one over here, on the bank of the river, and the other over there, on the other bank of the river.
Sa’an nan ni, Daniyel, na duba, a gabana kuwa ga waɗansu mutum biyu tsaye, ɗaya a wannan hayen kogi ɗaya kuma a ƙetaren kogin.
6 And I said to the man, who was clothed in linen, who stood over the waters of the river, “How long will it be until the end of these wonders?”
Ɗayansu ya ce wa mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, “Har yaushe waɗannan abubuwan banmamakin za su cika?”
7 And I heard the man, who was clothed in linen, who stood over the waters of the river, when he had lifted his right hand and his left hand up to heaven, and had sworn by He who lives forever, that it would be for a time, and times, and half a time. And when the dispersion of the hand of the holy people is completed, all these things will be completed.
Mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, ya ɗaga hannun damansa da kuma na hagunsa sama, sai na ji yana rantsuwa da wannan da yake raye har abada, yana cewa, “Zai kasance na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci. Za a kammala waɗannan abubuwa, sa’ad da aka gama ragargaje ikon tsarkakan mutane.”
8 And I heard and did not understand. And I said, “My lord, what will be after these things?”
Na kuma ji, amma ban fahimta ba. Don haka sai na yi tambaya, “Ranka yă daɗe, mene ne ƙarshen waɗannan abubuwa?”
9 And he said, “Go, Daniel, for the words are closed and sealed until the predetermined time.
Sai ya amsa ya ce, “Ka kama hanyarka, Daniyel, domin a rufe kalmomin aka kuma liƙe su har sai ƙarshen lokaci.
10 Many will be chosen and purified, and, as if by fire, they will be tested, and the impious will act impiously, and none of the impious will understand, yet the teachers will understand.
Za a tsarkake mutane da yawa, za a maishe su marasa aibi a kuma tace su; amma mugaye za su ci gaba da mugunta. Babu wani mugun da zai fahimta, amma waɗanda za su zama masu hikima za su fahimta.
11 And from the time when the continual sacrifice will be taken away and the abomination of desolation will be set up, there will be one thousand two hundred ninety days.
“Daga lokacin da za a hana miƙa hadayar ƙonawa ta yau da kullum, a kuma kafa abin banƙyama, wanda yake lalatarwa, za a yi kwana 1,290.
12 Blessed is he who waits and reaches until one thousand three hundred thirty-five days.
Mai albarka ne wanda ya jira har yă zuwa ƙarshen kwanakin nan 1,335.
13 But you, go, until the predetermined time, and you will rest and will stand in your allotted place at the end of days.
“Gare ka dai, ka yi tafiyarka har zuwa ƙarshe. Za ka huta, sa’an nan a ƙarshen kwanaki za ka tashi don karɓi sashen gadon da aka ba ka.”

< Daniel 12 >