< Genesis 41 >

1 After two years, Pharaoh saw a dream. He thought himself to be standing above a river,
Bayan shekaru biyu cif, Fir’auna ya yi mafarki. A mafarkin, ya ga yana tsaye kusa da Nilu,
2 from which ascended seven cows, exceedingly beautiful and stout. And they pastured in marshy places.
sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
3 Likewise, another seven emerged from the river, filthy and thoroughly emaciated. And they pastured on the same bank of the river, in green places.
Bayansu, sai ga waɗansu shanu bakwai, munana, ramammu, suka fito daga Nilu, suka tsaya kusa da waɗancan masu ƙiban, a bakin kogin.
4 And they devoured those whose appearance and condition of body was so wonderful. Pharaoh, having been awakened,
Shanun nan da suke munana ramammu, suka cinye shanu bakwai nan masu ƙiba mulmul. Sai Fir’auna ya farka.
5 slept again, and he saw another dream. Seven ears of grain sprung up on one stalk, full and well-formed.
Ya sāke yin barci, sai ya yi mafarki na biyu; ya ga kawuna bakwai na dawa, ƙosassu masu kyau, suka yi girma a kara guda.
6 Likewise, other ears of grain, of the same number, rose up, thin and struck with blight,
Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai na dawa, suka fito sirara waɗanda iskar gabas ta sa suka yanƙwane.
7 devouring all the beauty of the first. Pharaoh, when he awakened after his rest,
Siraran dawan suka haɗiye kawuna bakwai nan ƙosassu masu kyau. Sai Fir’auna ya farka, ashe, mafarki ne.
8 and when morning arrived, being terrified with fear, sent to all the interpreters of Egypt and to all of the wise men. And when they were summoned, he explained to them his dream; but there was no one who could interpret it.
Da safe sai hankalinsa ya tashi, saboda haka sai ya aika a kawo dukan masu duba da masu hikima na Masar. Fir’auna ya faɗa musu mafarkansa, amma babu wanda ya iya ba shi fassararsu.
9 Then at last the chief cupbearer, remembering, said, “I confess my sin.
Sai shugaban masu shayarwa ya ce wa Fir’auna, “Yau an tuna mini da kāsawata.
10 The king, being angry with his servants, ordered me and the chief miller of grain to be forced into the prison of the leader of the military.
Sai ya ci gaba ya ce, Fir’auna ya taɓa husata da bayinsa, ya kuma jefa ni da shugaban masu tuya a cikin kurkuku a gidan shugaban masu tsaro.
11 There, in one night, both of us saw a dream presaging the future.
Kowannenmu ya yi mafarki a wani dare, kowane mafarki kuma ya kasance da ma’anarsa.
12 In that place, there was a Hebrew, a servant of the same commander of the military, to whom we explained our dreams.
To, wani saurayi, mutumin Ibraniyawa ya kasance a can tare da mu, bawan shugaban masu tsaro. Sai muka faɗa masa mafarkanmu, ya kuwa fassara mana su, yana ba wa kowane mutum fassarar mafarkinsa.
13 Whatever we heard was proven afterwards by the event of the matter. For I was restored to my office, and he was suspended on a cross.”
Abubuwan kuwa suka kasance daidai yadda ya fassara su gare mu; aka mai da ni a matsayina, ɗaya mutumin kuwa aka rataye shi.”
14 Immediately, by the king’s authority, Joseph was led out of prison, and they shaved him. And changing his apparel, they presented him to him.
Sai Fir’auna ya aika a kawo Yusuf, aka kuwa kawo shi da sauri daga kurkuku. Sa’ad da ya yi aski, ya kuma canja tufafinsa, sai ya zo gaban Fir’auna.
15 And he said to him, “I have seen dreams, and there is no one who can unfold them. I have heard that you are very wise at interpreting these.”
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Na yi mafarki, kuma babu wanda ya iya fassara shi. Amma na ji an ce sa’ad da ka ji mafarki, kana iya fassara shi.”
16 Joseph responded, “Apart from me, God will respond favorably to Pharaoh.”
Yusuf ya amsa wa Fir’auna ya ce, “Ba ni ne da iyawar ba, Allah zai iya ba wa Fir’auna amsar da yake nema.”
17 Therefore, Pharaoh explained what he had seen: “I thought myself to be standing on the bank of a river,
Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “A cikin mafarkina, na ga ina tsaye a bakin Nilu,
18 and seven cows climbed up from the river, exceedingly beautiful and full of flesh. And they grazed in a pasture of a marshy greenery.
sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
19 And behold, there followed after these, another seven cows, with such deformity and emaciation as I had never seen in the land of Egypt.
Bayansu kuma, sai ga waɗansu shanu bakwai suka fito ƙanjamammu, munana, ramammu. Ban taɓa ganin irin munanan shanu haka a cikin dukan ƙasar Masar ba.
20 These devoured and consumed the first,
Ramammun shanun nan munana, suka cinye shanun nan bakwai masu ƙiba da suka fito da fari.
21 giving no indication of being full. But they remained in the same state of emaciation and squalor. Awakening, but being weighed down into sleep again,
Amma ko bayan da suka cinye su, babu wanda zai iya faɗa cewa sun yi haka; suna nan dai munana kamar yadda suke a dā. Sai na farka.
22 I saw a dream. Seven ears of grain sprang up on one stalk, full and very beautiful.
“Har yanzu kuma, a cikin mafarkina na ga kawuna bakwai na dawa ƙosassu masu kyau, suna girma a kara guda.
23 Likewise, another seven, thin and struck with blight, rose up from the stalk.
Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai suka fito, yanƙwananne sirara waɗanda iskar gabas ta yanƙwane.
24 And they devoured the beauty of the first. I explained this dream to the interpreters, and there is no one who can unfold it.”
Siraran kawunan dawan nan suka haɗiye kawuna bakwai nan masu kyau. Na faɗa wannan wa masu duba, amma ba wanda ya iya fassara mini shi.”
25 Joseph responded: “The dream of the king is one. What God will do, he has revealed to Pharaoh.
Sai Yusuf ya ce wa Fir’auna, “Mafarkan Fir’auna, ɗaya ne. Allah ya bayyana wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
26 The seven beautiful cows, and the seven full ears of grain, are seven years of abundance. And so the force of the dreams is understood to be the same.
Shanu masu kyau nan, shekaru bakwai ne, kawunan dawa bakwai ƙosassun nan kuwa shekaru bakwai ne; mafarkan iri ɗaya ne.
27 Likewise, the seven thin and emaciated cows, which ascended after them, and the seven thin ears of grain, which were struck with the burning wind, are seven approaching years of famine.
Shanun nan ramammu, munana, da suka zo daga baya, shekaru bakwai ne, haka ma kawuna dawan nan shanyayyu da iskar gabas ta yanƙwane. Shekaru ne bakwai na yunwa.
28 These will be fulfilled in this order.
“Haka yake kamar yadda na faɗa wa Fir’auna cewa Allah ya nuna wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
29 Behold, there will arrive seven years of great fertility throughout the entire land of Egypt.
Shekaru bakwai na yalwar abinci suna zuwa a dukan ƙasar Masar,
30 After this, there will follow another seven years, of such great barrenness that all the former abundance will be delivered into oblivion. For the famine will consume all the land,
amma shekaru bakwai na yunwa za su biyo bayansu. Tsananin yunwar za tă sa a manta da dukan isashen abincin da aka samu a ƙasar Masar, yunwa kuwa za tă rufe dukan ƙasar.
31 and the greatness of this destitution will cause the greatness of the abundance to be lost.
Ba za a tuna da isashen abincin da aka samu a ƙasar ba, domin yunwar da za tă biyo baya za tă zama da tsanani ƙwarai.
32 Now, as to what you saw the second time, it is a dream pertaining to the same thing. It is an indication of its firmness, because the word of God shall be done, and it shall be completed swiftly.
Dalilin da aka ba wa Fir’auna mafarkan nan kashi biyu kuwa shi ne cewa Allah ya riga ya ƙaddara al’amarin. Allah zai aikata shi, ba da daɗewa ba.
33 Now therefore, let the king provide a wise and industrious man, and place him over the land of Egypt,
“Yanzu fa, bari Fir’auna yă nemi mutum mai basira da kuma hikima, yă sa shi yă shugabanci ƙasar Masar.
34 so that he may appoint overseers throughout all the regions. And let a fifth part of the fruits, throughout the seven fertile years
Bari Fir’auna yă naɗa komishinoni a kan ƙasar don su karɓi kashi ɗaya bisa biyar na girbin Masar a lokacin shekaru bakwai na yalwar abinci.
35 that now have already begun to occur, be gathered into storehouses. And let all the grain be stored away, under the power of Pharaoh, and let it be kept in the cities.
Ya kamata su tara dukan abincin waɗannan shekaru masu kyau da suke zuwa, su yi ajiyar hatsin a ƙarƙashin ikon Fir’auna, don a ajiye a birane don abinci.
36 And let it be prepared for the future famine of seven years, which will oppress Egypt, and then the land will not be consumed by destitution.”
Ya kamata a adana abincin nan don ƙasar, kāriya shekaru bakwai na yunwa, domin a yi amfani da shi a lokacin shekarun yunwan da za su zo wa Masar, saboda kada ƙasar ta lalace da yunwa.”
37 The counsel pleased Pharaoh and all his ministers.
Shirin ya yi wa Fir’auna da kuma dukan hafsoshinsa kyau.
38 And he said to them, “Would we be able to find another such man, who is full of the Spirit of God?”
Saboda haka Fir’auna ya tambaye su, “Za mu iya samun wani kamar wannan mutum, wannan wanda Ruhun Allah yake cikinsa?”
39 Therefore, he said to Joseph: “Because God has revealed to you all that you have said, would I be able to find anyone wiser and as much like you?
Sai Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Da yake Allah ya ba ka sanin dukan waɗannan, babu wani mai basira da kuma hikima kamar ka.
40 You will be over my house, and to the authority of your mouth, all the people will show obedience. Only in one way, in the throne of the kingdom, will I go before you.”
Za ka shugabanci fadata, kuma dukan mutanena za su zama a ƙarƙashinka. Da sarauta kaɗai zan fi ka girma.”
41 And again, Pharaoh said to Joseph, “Behold, I have appointed you over the entire land of Egypt.”
Saboda haka Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ga shi na sa ka zama shugaban dukan ƙasar Masar.”
42 And he took the ring from his own hand, and he gave it into his hand. And he clothed him with a robe of fine linen, and he placed a necklace of gold around his neck.
Sa’an nan Fir’auna ya zare zoben sarauta daga yatsarsa, ya sa shi a yatsan Yusuf. Ya sanya masa rigar lallausan lilin, ya kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa.
43 And he caused him to ascend upon his second swift chariot, with the herald proclaiming that everyone should bend their knee before him, and that they should know that he was governor over the entire land of Egypt.
Ya sa shi ya hau keken yaƙi a matsayi mai binsa na biyu, mutane kuwa suka yi shela a gabansa suna cewa, “A ba da hanya!” Ta haka ya sa shi shugaba a kan dukan ƙasar Masar.
44 Likewise, the king said to Joseph: “I am Pharaoh: apart from your authority, no one will move hand or foot in all the land of Egypt.”
Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ni ne Fir’auna, amma in ba tare da umarninka ba, ba wanda zai ɗaga hannu ko ƙafa a cikin dukan Masar.”
45 And he changed his name and called him, in the Egyptian tongue: ‘Savior of the world.’ And he gave him as a wife, Asenath, the daughter of Potiphera, priest of Heliopolis. And so Joseph went out into the land of Egypt.
Fir’auna ya ba wa Yusuf suna Zafenat-Faneya, ya kuma ba shi Asenat’yar Fotifera firist na On, ta zama matarsa. Yusuf kuwa ya zaga dukan ƙasar Masar.
46 (Now he was thirty years old when he stood in the sight of king Pharaoh.) And he traveled throughout the regions of Egypt.
Yusuf yana zuwa shekara talatin sa’ad da ya shiga hidimar Fir’auna sarkin Masar. Yusuf kuwa ya fita daga gaban Fir’auna, ya zaga ko’ina a Masar.
47 And the fertility of the seven years arrived. And when the grain fields were reduced to sheaves, these were gathered into the storehouses of Egypt.
A shekaru bakwai na yalwa, ƙasar ta ba da amfani mai yawa.
48 And now all the abundance of grain was stored away in every city.
Yusuf ya tattara dukan abincin da aka samu a waɗannan shekaru bakwai na yalwa a Masar, ya kuma yi ajiyarsu a cikin birane. A kowane birni, ya sa abincin da aka nome a kewayensa.
49 And there was such a great abundance of wheat that it was comparable to the sands of the sea, and its bounty exceeded all measure.
Sai Yusuf ya tara hatsi da yawan gaske, kamar yashi a bakin teku, har sai da ya kāsa iya auna shi, gama ba a iya aunawa.
50 Then, before the famine arrived, Joseph had two sons born, whom Asenath, the daughter of Potiphera, priest of Heliopolis, bore for him.
Kafin shekarun yunwa su zo, Asenat’yar Fotifera, firist na On, ta haifa wa Yusuf’ya’ya maza biyu.
51 And he called the name of the firstborn Manasseh, saying, “God has caused me to forget all my labors and the house of my father.”
Yusuf ya ba wa ɗansa na fari suna Manasse ya ce, “Gama Allah ya sa na mance dukan wahalata da dukan gidan mahaifina.”
52 Likewise, he named the second Ephraim, saying, “God has caused me to increase in the land of my poverty.”
Ya ba wa ɗansa na biyu suna Efraim ya ce, “Gama Allah ya wadata ni cikin wahalata.”
53 And so, when the seven years of fertility that occurred in Egypt had passed,
Shekaru bakwai na yalwa a Masar suka zo ga ƙarshe,
54 the seven years of destitution, which Joseph had predicted, began to arrive. And the famine prevailed throughout the whole world, but there was bread in all the land of Egypt.
sai shekaru bakwai na yunwa suka soma shigowa, kamar yadda Yusuf ya faɗa. Aka yi yunwa ko’ina amma ban da ƙasar Masar. Don akwai abinci.
55 And being hungry, the people cried out to Pharaoh, asking for provisions. And he said to them: “Go to Joseph. And do whatever he will tell you.”
Sa’ad da dukan Masar ta fara jin yunwa, sai mutane suka yi wa Fir’auna kuka don abinci. Sai Fir’auna ya ce wa dukan Masarawa, “Ku tafi wurin Yusuf, ku kuma yi abin da ya faɗa muku.”
56 Then the famine increased daily in all the land. And Joseph opened all of the storehouses and sold to the Egyptians. For the famine had oppressed them also.
Sa’ad da yunwa ta bazu a dukan ƙasar, sai Yusuf ya buɗe gidajen ajiya, ya kuma sayar da hatsi ga Masarawa, gama yunwa ta yi tsanani a dukan Masar.
57 And all the provinces came to Egypt, to buy food and to temper the misfortune of their destitution.
Dukan ƙasashe kuwa suka zo Masar don saya hatsi daga Yusuf, gama yunwa ta yi tsanani a dukan duniya.

< Genesis 41 >