< Genesis 40 >

1 While these things were going on, it happened that two eunuchs, the cupbearer of the king of Egypt, and the miller of grain, offended their lord.
Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
2 And Pharaoh, being angry with them, (now the one was in charge of the cupbearers, the other of the millers of grain)
Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
3 sent them to the prison of the leader of the military, in which Joseph also was a prisoner.
ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
4 But the keeper of the prison delivered them to Joseph, who ministered to them also. Some little time passed by, while they were held in custody.
Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
5 And they both saw a similar dream on one night, whose interpretations should be related to one another.
sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
6 And when Joseph had entered to them in the morning, and had seen them sad,
Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
7 he consulted them, saying, “Why is your expression sadder today than usual?”
Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
8 They responded, “We have seen a dream, and there is no one to interpret it for us.” And Joseph said to them, “Doesn’t interpretation belong to God? Recount for me what you have seen.”
Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
9 The chief cupbearer explained his dream first. “I saw before me a vine,
Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
10 on which were three shoots, which grew little by little into buds, and, after the flowers, it matured into grapes.
kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
11 And the cup of Pharaoh was in my hand. Therefore, I took the grapes, and I pressed them into the cup that I held, and I handed the cup to Pharaoh.”
Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
12 Joseph responded: “This is the interpretation of the dream. The three shoots are the next three days,
Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
13 after which Pharaoh will remember your service, and he will restore you to your former position. And you will give him the cup according to your office, as you were accustomed to do before.
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
14 Only remember me, when it will be well with you, and do me this mercy, to suggest to Pharaoh to lead me out of this prison.
Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
15 For I have been stolen from the land of the Hebrews, and here, innocently, I was cast into the pit.”
Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
16 The chief miller of grain, seeing that he had wisely unraveled the dream, said: “I also saw a dream: that I had three baskets of meal above my head,
Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
17 and in one basket, which was the highest, I carried all foods that are made by the art of baking, and the birds ate from it.”
A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
18 Joseph responded: “This is the interpretation of the dream. The three baskets are the next three days,
Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
19 after which Pharaoh will carry away your head, and also suspend you from a cross, and the birds will tear your flesh.”
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
20 The third day thereafter was the birthday of Pharaoh. And making a great feast for his servants, he remembered, during the banquet, the chief cupbearer and the chief miller of grain.
To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
21 And he restored the one to his place, to present him the cup;
Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
22 the other he hanged on a gallows, and thus the truth of the interpreter of dreams was proven.
amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
23 And although he advanced with so much prosperity, the chief cupbearer forgot his interpreter of dreams.
Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.

< Genesis 40 >