< Genesis 17 >

1 In truth, after he began to be ninety-nine years of age, the Lord appeared to him. And he said to him: “I am the Almighty God. Walk in my sight and become complete.
Sa’ad da Abram ya yi shekaru 99, sai Ubangiji ya bayyana a gare shi ya ce, ni “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi tafiya a gabana ka kuma zama marar abin zargi.
2 And I will set my covenant between me and you. And I will multiply you very exceedingly.”
Zan tabbatar da alkawarina tsakanina da kai, zan kuma ƙara zuriyarka ta yi yawa.”
3 Abram fell prone on his face.
Abram ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, Allah kuma ya ce masa,
4 And God said to him: “I AM, and my covenant is with you, and you will be the father of many nations.
“Gare ni kam, wannan shi ne alkawarina da kai, za ka zama mahaifin al’ummai masu yawa.
5 No longer will your name be called Abram. But you will be called Abraham, for I have established you as the father of many nations.
Ba za a ƙara kiranka Abram ba; sunanka zai zama Ibrahim, gama na mai da kai uban al’ummai masu yawa.
6 And I will cause you to increase very greatly, and I will set you among the nations, and kings will come forth from you.
Zan sa ka azurta sosai, zan yi al’ummai daga cikinka, sarakuna kuma za su fito daga cikinka,
7 And I will establish my covenant between me and you, and with your offspring after you in their generations, by a perpetual covenant: to be God to you and to your offspring after you.
zan kafa alkawarina kamar madawwamin alkawari tsakanina da kai da kuma zuriyarka bayanka har tsararraki masu zuwa, in zama Allahnka da kuma Allahn zuriyarka a bayanka.
8 And I will give to you and to your offspring, the land of your sojourn, all the land of Canaan, as an eternal possession, and I will be their God.”
Dukan ƙasar Kan’ana inda kake baƙo a yanzu, zan ba da ita a matsayin madawwamiyar mallaka gare ka da kuma zuriyarka a bayanka, zan kuma zama Allahnsu.”
9 Again God said to Abraham: “And you therefore shall keep my covenant, and your offspring after you in their generations.
Sa’an nan Allah ya ce wa Ibrahim. “Kai fa, sai ka kiyaye alkawarina, kai da zuriyarka bayanka, har tsararraki masu zuwa.
10 This is my covenant, which you shall observe, between me and you, and your offspring after you: All the males among you shall be circumcised.
Wannan shi ne alkawarina da kai da kuma zuriyarka a bayanka, alkawarin da za ka kiyaye ke nan. Kowane namiji a cikinku kuwa za a yi masa kaciya.
11 And you shall circumcise the flesh of your foreskin, so that it may be a sign of the covenant between me and you.
Za ku yi kaciya, za tă kuma zama alamar alkawari tsakanina da kai.
12 An infant of eight days will be circumcised among you, every male in your generations. So also servants born to you, as well as those bought, shall be circumcised, even those who are not of your stock.
Daga yanzu duk namijin da aka haifa a cikinku za a yi masa kaciya a rana ta takwas har dukan zamananku, ko haifaffen gida ne, ko sayayye da kuɗi daga kowane baƙo wanda ba na zuriyarku ba.
13 And my covenant shall be with your flesh as an eternal covenant.
Ko haifaffe a gidanka ko an sayo da kuɗi, dole a yi musu kaciya. Alkawarina cikin jikinku zai kasance madawwamin alkawari.
14 The male, the flesh of whose foreskin will not be circumcised, that soul shall be eliminated from his people. For he has made my covenant void.”
Kowane namijin da ba a yi masa kaciya a jiki ba, za a fid da shi daga cikin mutanensa; domin ya karya alkawarina.”
15 God said also to Abraham: “Your wife Sarai, you shall not call Sarai, but Sarah.
Allah ya kuma ce wa Ibrahim, “Game da Saira matarka kuwa, ba za ka ƙara kiranta Saira ba, sunanta zai zama Saratu.
16 And I will bless her, and from her I will give you a son, whom I will bless, and he will be among the nations, and the kings of the peoples will rise from him.”
Zan sa mata albarka, ban da haka ma, zan ba ka ɗa ta wurinta, zan sa mata albarka, za tă kuwa zama mahaifiyar al’ummai; sarakunan mutane za su fito daga gare ta.”
17 Abraham fell on his face, and he laughed, saying in his heart: “Do you think a son can be born to a one hundred year old man? And will Sarah give birth at the age of ninety?”
Ibrahim ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, ya yi dariya, ya ce wa kansa, “Za a haifi ɗa wa mutum mai shekaru ɗari? Saratu za tă haifi ɗa tana da shekaru tasa’in?”
18 And he said to God, “If only Ishmael would live in your sight.”
Ibrahim ya kuma ce wa Allah, “Me zai hana a dai bar Ishmayel kawai yă gāji alkawarin nan da ka yi mini.”
19 And God said to Abraham: “Your wife Sarah shall give birth to a son, and you shall call his name Isaac, and I will establish my covenant with him as a perpetual covenant, and with his offspring after him.
Sai Allah ya ce, “Duk da haka dai, matarka Saratu za tă haifi maka ɗa; za ka kuma kira shi Ishaku. A kansa zan tabbatar da madawwamin alkawarina, da kuma ga zuriyarsa da za su zo bayansa.
20 Likewise, concerning Ishmael, I have heard you. Behold, I will bless and enlarge him, and I will multiply him greatly. He will produce twelve leaders, and I will make him into a great nation.
Game da Ishmayel kuwa, na ji ka. Tabbatacce zan albarkace shi, zan sa yă azurta, zai kuma ƙaru ƙwarai. Zai zama mahaifin masu mulki goma sha biyu, zan kuma maishe shi babban al’umma!
21 Yet in truth, I will establish my covenant with Isaac, to whom Sarah will give birth for you at this time next year.”
Amma dai zan kafa alkawarina da Ishaku wanda Saratu za tă haifa maka war haka shekara mai zuwa.”
22 And when he had finished speaking with him, God ascended from Abraham.
Da ya gama magana da Ibrahim, sai Allah ya tashi daga gare shi.
23 Then Abraham took his son Ishmael, and all who were born in his house, and all whom he had bought, every male among the men of his house, and he circumcised the flesh of their foreskin promptly, the very same day, just as God had instructed him.
A wannan rana, Ibrahim ya ɗauki ɗansa Ishmayel da dukan waɗanda aka haifa cikin gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗinsa, ya kuwa yi wa kowane namiji a cikin gidansa kaciya kamar yadda Allah ya faɗa masa.
24 Abraham was ninety-nine years old when he circumcised the flesh of his foreskin.
Ibrahim yana da shekara tasa’in da tara sa’ad da aka yi masa kaciya,
25 And his son Ishmael had completed thirteen years at the time of his circumcision.
Ishmayel ɗansa kuma yana da shekara goma sha uku.
26 On the very same day, Abraham was circumcised with his son Ishmael.
Aka yi wa Ibrahim da ɗansa Ishmayel kaciya a rana ɗaya.
27 And all the men of his house, those born in his house, as well as those who were bought, even the foreigners, were circumcised with him.
Aka yi wa kowane namiji a gidan Ibrahim kaciya, da waɗanda aka haifa a gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗi daga baƙo.

< Genesis 17 >