< Ezra 5 >

1 Now Haggai, the prophet, and Zechariah, the son of Iddo, prophesying to the Jews who were in Judea and Jerusalem, prophesied in the name of the God of Israel.
Sai annabi Haggai, da annabi Zakariya zuriyar Iddo, suka yi wa Yahudawa a Yahuda da Urushalima annabci a cikin sunan Allah na Isra’ila wanda yake da mulki a kansu.
2 Then Zerubbabel, the son of Shealtiel, and Jeshua, the son of Jozadak, rose up and began to build the temple of God in Jerusalem. And the prophets of God were with them, assisting them.
Sa’an nan Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da Yeshuwa ɗan Yozadak suka yi shiri suka kama aikin sāke gina gidan Allah a Urushalima. Annabawan Allah kuwa suna tare da su, suna taimakonsu.
3 Then, at the same time, Tattenai, who was the governor beyond the river, and Shetharbozenai, and their counselors came to them. And they spoke in this way to them: “Who has given you counsel, so that you would build this house and repair its walls?”
A wannan lokaci, Tattenai gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu suka je wurinsu suka tambaye su cewa, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali har ku gyara katangar?”
4 We responded to this by giving them the names of the men who were the founders of that building.
Suka kuma tambaye su “Ina sunayen waɗanda suke wannan gini?”
5 But the eye of their God was set over the elders of the Jews, and so they were unable to hinder them. And it was agreed that the matter should be referred to Darius, and then they would give a reply against that accusation.
Amma Allah yana tsaron dattawan Yahudawa, saboda haka ba a hana su aikin ba har sai rahoto ya kai wurin Dariyus aka kuma sami amsarsa a rubuce tukuna.
6 A copy of the letter that Tattenai, the governor of the region beyond the river, and Shetharbozenai, and his counselors, the rulers who were beyond the river, sent to Darius the king.
Ga wasiƙar da Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu masu riƙe da muƙamai a Kewayen Kogin Yuferites suka aika wa Sarki Dariyus.
7 The word that they sent him was written in this way: “To Darius, the king of all peace.
Ga rahoton da suka aika masa. Zuwa ga Sarki Dariyus. Gaisuwa da fatan alheri.
8 Let it be known to the king, that we went to the province of Judea, to the house of the great God, which they are building with rough stones, and with timber set into the walls. And this work is being built up diligently, and it increases by their hands.
Ya kamata sarki yă sani cewa mun je yankin Yahuda, zuwa gidan Allah mai girma. Muka ga mutanen suna ginin haikalin da manyan duwatsu, suna sa katakai a bangon. Ana aikin da ƙwazo, aikin kuma yana cin gaba sosai, suna kuma lura da shi.
9 Therefore, we questioned those elders, and we spoke to them in this way: ‘Who has given authority to you, so that you would build this house and repair these walls?’
Mun tambayi dattawan muka ce musu, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali, ku kuma sāke gyara katangarsa?”
10 But we also required of them their names, so that we might report to you. And we have written down the names of their men, those who are leaders among them.
Muka kuma tambaye su sunayensu don mu rubuta mu sanar da kai waɗanda suke shugabanninsu.
11 Then they responded a word to us in this manner, saying: ‘We are the servants of the God of heaven and earth. And we are building the temple that was constructed these many years before, and which a great king of Israel had built and constructed.
Wannan ita ce amsar da suka ba mu. “Mu bayin Allah na sama da ƙasa ne, muna sāke gina haikalin da aka gina tun shekaru da yawa da suka wuce, da wani babban sarkin Isra’ila ya gina ya kuma gama.
12 But afterward, our fathers had provoked the God of heaven to wrath, so he delivered them into the hands of Nebuchadnezzar, the king of Babylon, the Chaldean. And he destroyed this house, and he transferred its people to Babylon.
Amma domin kakanninmu sun ɓata wa Allah na sama rai, sai ya bari suka fāɗa cikin hannun Nebukadnezzar mutumin Kaldiya, sarkin Babilon, wanda ya rushe wannan haikali, ya kuma kwashe mutane zuwa Babilon.
13 Then, in the first year of Cyrus, the king of Babylon, king Cyrus issued a decree, so that this house of God would be built.
“Duk da haka, a shekara ta farko ta mulkin Sairus sarkin Babilon, Sarki Sairus ya ba da umarni cewa a sāke gina wannan gidan Allah.
14 And now the vessels of gold and silver from the temple of God, which Nebuchadnezzar had taken from the temple that was in Jerusalem, and which he had carried away to the temple of Babylon, king Cyrus brought out of the temple of Babylon, and they were given to one called Sheshbazzar, whom he also appointed as governor.
Ya kuma kwashe kwanonin zinariya da azurfa na gidan Allah daga haikalin Babilon waɗanda Nebukadnezzar ya kwasa daga haikali a Urushalima. Sa’an nan sarki Sairus ya ba wa wani mutum mai suna Sheshbazzar umarni wanda ya sa ya zama gwamna,
15 And he said to him: “Take these vessels, and go, and set them in the temple that is in Jerusalem. And let the house of God be built in its place.”
ya ce masa, ‘Ka kwashe kayan nan ka je ka zuba su a cikin haikalin Allah a Urushalima. Ka kuma sāke gina gidan Allah a wurin da yake a dā.’
16 And so this same Sheshbazzar then came and set the foundations of the temple of God in Jerusalem. And from that time, even until now, it is being built, and it is not yet completed.’
“Saboda haka Sheshbazzar ya so ya aza harsashin gina gidan Allah a Urushalima. Tun daga wancan lokaci har zuwa yau ana kan gina shi amma ba a gama ba.”
17 Now then, if it seems good to the king, let him search in the king’s library, which is in Babylon, to see whether it was ordered by king Cyrus, that the house of God in Jerusalem should be built. And may the will of the king be sent to us about this matter.”
Yanzu in sarki yana so, bari a duba cikin littattafan tarihi na sarakuna na Babilon a gani ko lalle sarki Sairus ya ba da umarni a sāke gina gidan Allah a Urushalima. Bari sarki yă aiko mana da abin da ya gani game da wannan abu.

< Ezra 5 >