< 2 Chronicles 1 >

1 Then Solomon, the son of David, was strengthened in his reign, and the Lord his God was with him, and he magnified him on high.
Solomon ɗan Dawuda ya kafa kansa sosai a bisa masarautarsa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi ya kuma sa ya zama mai girma sosai.
2 And Solomon instructed the whole of Israel, the tribunes, and the centurions, and the rulers, and the judges over all of Israel, and the leaders of the families.
Sai Solomon ya yi magana ga dukan Isra’ila, ga shugabannin mayaƙa dubu-dubu da shugabannin mayaƙa ɗari-ɗari, ga alƙalai da kuma ga dukan shugabanni a Isra’ila, kawunan iyalai,
3 And he went away with the entire multitude to the high place of Gibeon, where the tabernacle of the covenant of the Lord was, which Moses, the servant of God, made in the wilderness.
Solomon tare da dukan taron suka tafi masujadan kan tudu a Gibeyon, gama Tentin Sujadar Allah yana can, wanda Musa bawan Ubangiji ya yi a hamada.
4 For David had brought the ark of God from Kiriath-jearim, to the place that he had prepared for it, and where he had pitched a tabernacle for it, that is, in Jerusalem.
Dawuda ya riga ya haura da akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim zuwa inda ya shirya dominsa, domin yă kafa masa tenti a Urushalima.
5 Also, the altar of brass, which Bezalel, the son of Uri, the son of Hur, had constructed, was there before the tabernacle of the Lord. And so Solomon sought it, with the entire assembly.
Amma bagaden tagullar da Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, ya yi a Gibeyon a gaba tabanakul na Ubangiji; saboda haka Solomon da taron suka neme nufin Ubangiji a can.
6 And Solomon ascended to the bronze altar, before the tabernacle of the covenant of the Lord, and he offered upon it one thousand victims.
Solomon ya haura zuwa bagaden tagulla a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada, ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa dubbai a kansa.
7 But behold, during that night God appeared to him, saying, “Request what you wish, so that I may give it to you.”
A wannan dare Allah ya bayyana ga Solomon, ya ce masa, “Roƙi duk abin da kake so in ba ka.”
8 And Solomon said to God: “You have shown great mercy to my father David. And you have appointed me as king in his place.
Solomon ya amsa wa Allah, “Ka nuna alheri mai girma ga Dawuda mahaifina ka kuma naɗa ni sarki a matsayinsa.
9 Now therefore, O Lord God, let your word be fulfilled, which you promised to my father David. For you have made me king over your great people, who are as innumerable as the dust of the earth.
To, yanzu, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi ga mahaifina Dawuda yă tabbata, gama ka naɗa ni sarki a bisa mutanen da suka wuce ƙirge kamar ƙurar ƙasa.
10 Give to me wisdom and understanding, so that I may enter and depart before your people. For who is able worthily to judge this, your people, who are so great?”
Ka ba ni hikima da sani, don in iya jagorance wannan mutane, gama wa zai iya shugabance wannan jama’arka mai girma?”
11 Then God said to Solomon: “Since this is the choice that pleased your heart, and you did not request wealth and substance and glory, nor the lives of those who hate you, nor even many days of life, since instead you requested wisdom and knowledge so that you may be able to judge my people, over whom I have appointed you as king:
Allah ya ce wa Solomon, “Da yake wannan ne sha’awar zuciyarka, ba ka kuwa nemi wadata, arziki ko girma ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, da yake kuma ba ka nemi tsawon rai ba, amma ka nemi hikima da sani don ka shugabanci jama’ata wadda na naɗa ka sarki,
12 wisdom and knowledge are granted to you. And I will give to you wealth and substance and glory, so that none of the kings either before you or after you will be similar to you.”
saboda haka za a ba ka hikima da sani. Zan kuma ba ka wadata, arziki da girma, waɗanda babu wani sarki kafin kai da ya taɓa kasance da su kuma babu wani a bayanka da zai kasance da su.”
13 Then Solomon went from the high place of Gibeon to Jerusalem, before the tabernacle of the covenant, and he reigned over Israel.
Sa’an nan Solomon ya tafi Urushalima daga masujadar kan tudu a Gibeyon, da kuma daga gaban Tentin Sujada. Ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila.
14 And he gathered to himself chariots and horsemen. And they brought to him one thousand four hundred chariots, and twelve thousand horsemen. And he caused them to be in the cities of the chariots, and with the king in Jerusalem.
Solomon ya tara kekunan yaƙi da dawakai, ya kasance da kekunan yaƙi dubu da ɗari huɗu da kuma dawakai dubu goma sha biyu, waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi, da kuma tare da shi a Urushalima.
15 And the king offered silver and gold in Jerusalem as if they were stones, and cedar trees as if they were sycamores, which grow in the plains in a great multitude.
Sarki ya sa azurfa da zinariya suka zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
16 Then horses were brought to him from Egypt and from Kue, by the negotiators of the king, who went and bought for a price:
Aka shigo da dawakan Solomon daga Masar da kuma daga Kuye’yan kasuwan fada suka saye su daga Kuye.
17 a four-horse chariot for six hundred pieces of silver, and a horse for one hundred fifty. A similar offer to purchase was made known among all the kingdoms of the Hittites, and among the kings of Syria.
Suka shigo da kekunan yaƙi daga Masar a kan shekel ɗari shida-shida na azurfa, doki kuma a kan shekel ɗari da hamsin-hamsin. Suka kuma riƙa fitar da su ƙasashen waje zuwa dukan sarakunan Hittiyawa da na Arameyawa.

< 2 Chronicles 1 >