< Ezra 4 >

1 Now the enemies of Judah and of Benjamin heard that the sons of the captivity were building a temple to the Lord, the God of Israel.
Sa’ad da abokan gāban Yahuda da na Benyamin suka ji cewa waɗanda suka dawo daga bauta suna gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila
2 And so, drawing near to Zerubbabel and to the leaders of the fathers, they said to them: “Let us build with you, for we seek your God just as you do. Behold, we have immolated victims to him from the days of Esarhaddon, king of Assyria, who brought us here.”
sai suka zo wurin Zerubbabel da kuma wurin shugabannin iyalai, suka ce, “Bari mu taimake ku ginin domin mu ma muna addu’a ga Allahnku yadda kuke yi, muna miƙa masa hadaya tun lokacin Esar-Haddon sarkin Assuriya wanda ya kawo mu nan.”
3 And Zerubbabel, and Jeshua, and the rest of the leaders of the fathers of Israel said to them: “It is not for you to build the house of our God with us. Instead, we alone shall build to the Lord our God, just as Cyrus, the king of the Persians, has commanded us.”
Amma Zerubbabel, Yeshuwa, da sauran shugabannin iyalai na Isra’ila suka amsa suka ce, “Ba za ku sa hannu cikin gina wa Allahnmu haikali ba, mu kaɗai za mu gina wa Ubangiji, Allah na Isra’ila gini kamar yadda Sarki Sairus, sarkin Farisa, ya umarce mu.”
4 Therefore, it happened that the people of the land impeded the hands of the people of Judah, and they troubled them in building.
Sai mutanen da suke zama a wurin suka fara yin ƙoƙari su sa mutanen Yahuda su karaya, suka sa su ji tsoron ci gaba da ginin.
5 Then they hired counselors against them, so that they might argue against their plan during all the days of Cyrus, king of Persia, even until the reign of Darius, king of the Persians.
Suka yi hayar mashawarta don su ga cewa sun ɓata ƙoƙarinsu dukan kwanakin mulkin Sairus sarkin Farisa har zuwa kwanakin mulkin Dariyus sarkin Farisa.
6 And so, during the reign of Ahasuerus, at the beginning of his reign, they wrote an accusation against the inhabitants of Judah and of Jerusalem.
A farkon mulkin Zerzes, sai abokan gāba suka kawo ƙarar mutanen Yahuda da na Urushalima.
7 And so, in the days of Artaxerxes, Bishlam, Mithredath, and Tabeel, and the others who were in their council wrote to Artaxerxes, king of the Persians. Now the letter of accusation was written in Syriac, and was being read in the Syrian language.
A zamanin Artazerzes sarkin Farisa kuma, sai Bishlam, da Mitredat, da Tabeyel, da sauran abokansu suka rubuta wasiƙa zuwa ga Artazerzes. Aka rubuta wasiƙar da harufan Arameyik, aka kuma fassara ta a yaren Arameyik.
8 Rehum, the commander, and Shimshai, the scribe, wrote one letter from Jerusalem to king Artaxerxes, in this manner:
Rehum shugaban rundunar soja, da Shimshai marubuci, suka rubuta wasiƙar a kan Urushalima zuwa ga sarki Artazerzes, suka ce.
9 “Rehum, the commander, and Shimshai, the scribe, and the rest of their counselors, the judges, and rulers, the officials, those from Persia, from Erech, from Babylonia, from Susa, the Dehavites, and the Elamites,
Rehum shugaban sojoji, da Shimshai marubuci, da sauran abokansu, wato, alƙalai, da masu riƙe da muƙamai daga Farisa, Uruk da Babilon, mutanen Elam da na Shusha,
10 and the rest of the nations, whom the great and glorious Osnappar transferred and caused to live in the cities of Samaria and in the rest of the regions across the river in peace:
da sauran mutane waɗanda mai girma Osnaffar ya kwaso, ya zaunar da su cikin birnin Samariya da sauran wurare na Kewayen Kogin Yuferites.
11 to king Artaxerxes. (This is a copy of the letter, which they sent to him.) Your servants, the men who are across the river, send a greeting.
(Ga abin da suka rubuta.) Zuwa ga sarki Artazerzes. Daga bayinka, mutanen Kewayen Kogin Yuferites.
12 Let it be known to the king, that the Jews, who ascended from you to us, have arrived in Jerusalem, a rebellious and most wicked city, which they are building, constructing its ramparts and repairing the walls.
Ya kamata sarki ya san cewa Yahudawan da suka hauro wurinmu daga wurinka, sun je Urushalima suna sāke gina wannan mugun birni mai tawaye. Suna sāke gyara katangar, suna kuma gyara harsashin katangar.
13 And now let be it known to the king, that if this city will have been built up, and its walls repaired, they will not pay tribute, nor tax, nor yearly revenues, and this loss will affect even the kings.
Ya kamata fa, sarki ya san cewa in aka sāke gina wannan birni duk da katangar birnin, mutanen birnin ba za su dinga biyan haraji, da kuɗin shiga, da na fitar da kaya ba, wannan zai sa aljihun masarauta yă bushe.
14 But, remembering the salt that we have eaten in the palace, and because we are led to believe that it is a crime to see the king harmed, we have therefore sent and reported to the king,
Tun da yake muna ƙarƙashin fada, bai kyautu mu bari a rena sarki ba, Saboda haka muke sanar da sarki,
15 so that you may search in the books of the histories of your fathers, and you may find written in the records, and you may know that this city is a rebellious city, and that it is harmful to the kings and the provinces, and that wars were incited within it from the days of antiquity. For which reason also, the city itself was destroyed.
domin a bincika a littattafan tarihin kakanninka. Za ka ga cewa wannan birni mai tawaye ne. Tun daga zamanin dā wannan birnin yana ba sarakuna da yankuna damuwa. Wannan ne ya sa aka ragargazar da birnin.
16 We report to the king that if this city will have been built, and its walls repaired, you will have no possession across the river.”
Muna sanar da sarki cewa in har aka sāke gina wannan birnin da katangarsa, zai zama ka rasa kome a gefen Kewayen Kogin Yuferites ke nan.
17 The king sent word to Rehum, the commander, and to Shimshai, the scribe, and to the rest who were in their council, to the inhabitants of Samaria, and to the others across the river, offering a greeting and peace.
Sarki ya aika da wannan amsa. Zuwa ga Rehum shugaban sojoji, Shimshai marubuci da kuma sauran abokansu waɗanda suke zama a Samariya da kuma sauran wurare a Kewayen Kogin Yuferites. Gaisuwa.
18 “The accusation, which you have sent to us, has been read aloud before me.
An karanta, an kuma fassara mini wasiƙar da kuma aika.
19 And it was commanded by me, and they searched and found that this city, from the days of antiquity, has rebelled against the kings, and that seditions and battles have been incited within it.
Na ba da umarni aka kuma yi bincike, aka tarar cewa wannan birni ya daɗe yana yi wa sarakuna tawaye, an yi tashin hankali a birnin.
20 Then too, there have been very strong kings in Jerusalem, who also ruled over the entire region which is across the river. They have also taken tribute, and tax, and revenues.
Urushalima ta yi sarakuna masu iko sosai waɗanda suka yi mulkin Kewayen Kogin Yuferites gaba ɗaya, an kuma biya masu haraji, da kuɗin shiga da na fita na kaya.
21 Now therefore, hear the sentence: Prohibit those men, so that this city may be not built, until perhaps there may be further orders from me.
Saboda haka sai ku ba da umarni yanzu cewa mutanen su daina wannan aiki sai lokacin da na ba da umarni.
22 See to it that you are not negligent in fulfilling this, otherwise, little by little, the evil may increase against the kings.”
Ku tabbata ka ɗauki wannan da muhimmanci. Don me za a bari wannan abu yă zama abin damuwa ga sarauta?
23 And so a copy of the edict of king Artaxerxes was read before Rehum, the commander, and Shimshai, the scribe, and their counselors. And they went away hurriedly to Jerusalem, to the Jews. And they prohibited them by force and by strength.
Da gama karanta wasiƙar sarki Artazerzes wa Rehum da Shimshai marubuci, da abokansu, sai suka yi sauri suka je wurin Yahudawa a Urushalima, suka hana su aikin ƙarfi da yaji.
24 Then the work of the house of the Lord in Jerusalem was interrupted, and it did not resume until the second year of the reign of Darius, the king of the Persians.
Saboda haka aikin a gidan Allah a Urushalima ya tsaya cik sai a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus sarkin Farisa.

< Ezra 4 >