< Ezra 3 >

1 And now the seventh month had arrived, and the sons of Israel were in their cities. Then, the people were gathered together, like one man, in Jerusalem.
Da tsayawar watan bakwai, sai Isra’ilawa waɗanda suka koma garuruwansu suka taru da nufi ɗaya a Urushalima.
2 And Jeshua, the son of Jozadak, rose up with his brothers, the priests. And Zerubbabel, the son of Shealtiel, rose up with his brothers. And they built the altar of the God of Israel, so that they might offer holocausts upon it, just as it was written in the law of Moses, the man of God.
Sai Yeshuwa ɗan Yozadak da sauran firistoci, da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da abokan aikinsa, suka fara gina bagaden Allah na Isra’ila don miƙa hadaya ta ƙonawa bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa mutumin Allah.
3 Now they set the altar of God upon its bases, while keeping the people of all the surrounding lands away from it. And they offered upon it a holocaust to the Lord, morning and evening.
Duk da tsoron da suke ji na mutanen da suke kewaye da su, sun gina bagaden a wurinsa, suka kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagaden ga Ubangiji safe da yamma.
4 And they kept the solemnity of tabernacles, just as it was written, and the holocaust of each day in order, according to the precept, the work of each day in its time.
Bisa ga abin da yake a rubuce kuma, suka yi biki Bikin Tabanakul, suka miƙa hadayu kowace rana gwargwadon yawan hadayun da ake bukata.
5 And after these, they offered the continual holocaust, as much on the new moons as on all the solemnities of the Lord that were consecrated, and on all those when a voluntary gift was offered to the Lord.
Bayan wannan, suka miƙa hadayu na ƙonawa yadda aka saba. Suka miƙa hadayu na Sabon Wata, da hadayu na bukukkuwan Ubangiji, da kuma hadayun da aka bayar da yardar rai ga Ubangiji.
6 From the first day of the seventh month, they began to offer holocausts to the Lord. But the temple of God had not yet been founded.
A ranar farko ta watan bakwai, sai suka fara miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko da yake ba a riga an aza harsashin ginin haikalin Ubangiji ba.
7 And so they gave money to those who cut and laid stones. Similarly, they gave food, and drink, and oil to the Sidonians and the Tyrians, so that they would bring cedar wood, from Lebanon to the sea at Joppa, in accord with what had been commanded of them by Cyrus, the king of the Persians.
Sai suka ba wa magina da kafintoci kuɗi, suka ba wa mutanen Sidon da na Taya abinci, da abin sha, da mai, don su kawo itatuwan al’ul a Yaffa daga Lebanon ta teku, yadda Sairus sarkin Farisa ya ba da umarni.
8 Then, in the second year of their advent to the temple of God in Jerusalem, in the second month, Zerubbabel, the son of Shealtiel, and Jeshua, the son of Jozadak, and the remainder of their brothers, the priests, and the Levites, and all who had arrived from the captivity to Jerusalem, began, and they appointed Levites, from twenty years and over, to hasten the work of the Lord.
A wata na biyu na shekara ta biyu, bayan sun komo gidan Allah a Urushalima, sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, Yoshuwa ɗan Yozadak da sauran’yan’uwansa (Firistoci da Lawiyawa da duk waɗanda suka komo Urushalima daga bauta) suka fara aiki, aka zaɓi Lawiyawa daga masu shekaru ashirin da haihuwa zuwa waɗanda suka wuce haka don su dubi aikin ginin gidan Ubangiji.
9 And Jeshua and his sons and his brothers, Kadmiel and his sons, and the sons of Judah, like one man, stood so that they might have charge over those who did the work in the temple of God: the sons of Henadad, and their sons, and their brothers, the Levites.
Yeshuwa da’ya’yansa maza, da’yan’uwansa, da Kadmiyel da’ya’yan Yahuda (’yan zuriyar Hodawiya), da’ya’yan Henadad, da’ya’yansu da’yan’uwansu, dukansu Lawiyawa ne, suka haɗa kai cikin duban masu aikin gidan Allah.
10 And when the builders had founded the temple of the Lord, the priests stood in their adornment with trumpets, and the Levites, the sons of Asaph, stood with cymbals, so that they might praise God by the hand of David, the king of Israel.
Da masu ginin suka aza harsashin ginin haikalin Ubangiji, sai firistoci suka sa kayansu na firistoci suka riƙe ƙahonin busa, Lawiyawa (’ya’yan Asaf) kuwa suka riƙe kuge, suka yi shiri domin su rera yabo ga Ubangiji kamar yadda Dawuda Sarkin Isra’ila ya ba da umarni.
11 And they sung together with hymns and confession to the Lord: “For he is good. For his mercy is over Israel unto eternity.” And likewise, all the people shouted with a great clamor in praise to the Lord, because the temple of the Lord had been founded.
Suka rera waƙar yabo da godiya ga Ubangiji, suna cewa, “Shi nagari ne; ƙaunarsa kuwa ga Isra’ila har abada ce.” Dukan jama’a kuwa suka yabi Ubangiji da murya mai ƙarfi, domin an aza harsashin ginin gidan Ubangiji.
12 And many of the priests and the Levites, and the leaders of the fathers and of the elders, who had seen the former temple, when now this temple was founded and was before their eyes, wept with a great voice. And many of them, shouting for joy, lifted up their voice.
Amma tsofaffin firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai da yawa, waɗanda dā suka ga yadda haikali na farko yake, suka fashe da kuka mai ƙarfi sa’ad da suka ga an aza harsashin ginin wannan haikali, yayinda waɗansu kuma suka yi ihu da farin ciki.
13 Neither could anyone distinguish between the voice of clamor of joy, and a voice of weeping of the people. For the shouting of the people mixed into a great clamor, and the voice was heard from far away.
Ba wanda zai iya rabe tsakanin ihun farin ciki da na kuka, domin mutanen sun tā da murya sosai har aka ji su daga nesa.

< Ezra 3 >