< Ezekiel 9 >

1 And he cried out in my ears with a loud voice, saying: “The visitations of the city have drawn near, and each one has equipment for killing in his hand.”
Sai na ji ya yi kira da babbar murya yana cewa, “Kawo matsaran birni a nan, kowanne da makami a hannunsa.”
2 And behold, six men were approaching from the way of the upper gate, which looks to the north. And each one had equipment for killing in his hand. Also, one man in their midst was clothed with linen, and an instrument for writing was at his waist. And they entered and stood beside the bronze altar.
Na kuma ga mutane shida suna zuwa daga kowane gefen ƙofar ta bisa, wadda take fuskantar arewa, kowanne da makamin kisa a hannunsa. Tare da su akwai mutum saye da lilin yana rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa. Suka shiga suka tsaya kusa da bagaden tagulla.
3 And the glory of the Lord of Israel was taken up, from the cherub upon which he was, to the threshold of the house. And he called out to the man who was clothed with linen and had an instrument for writing at his waist.
To, fa, ɗaukakar Allah na Isra’ila ta haura daga bisa kerubobi, inda ta kasance, ta tashi zuwa bakin madogarar ƙofar haikali. Sai Ubangiji ya kira mutumin da yake saye da lilin wanda ya rataye jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa
4 And the Lord said to him: “Cross through the middle of the city, in the center of Jerusalem, and seal a Tau upon the foreheads of the grieving men, who are mourning over all the abominations which are being committed in its midst.”
ya ce masa, “Ka ratsa birnin Urushalima ka sa shaida a goshin waɗanda suke baƙin ciki da kuma makoki a kan dukan abubuwan banƙyamar da ake yi a cikinsa.”
5 And he said to the others, in my hearing: “Cross through the city after him, and strike! Your eye shall not be lenient, and you shall not take pity.
Yayinda nake saurara, sai ya ce wa waɗansu, “Ku bi shi ta birnin ku kuma kashe, babu tausayi ko kuwa jinƙai.
6 Kill, even to utter destruction, old men, young men, and virgins, little ones, and women. But all upon whom you see the Tau, you shall not kill. And begin from my sanctuary.” Therefore, they began with the men among the elders, who were before the face of the house.
Ku kashe tsofaffi da samari da’yan mata, mata da yara, amma kada ku taɓa wani wanda yake da shaida. Ku fara a wuri mai tsarkina.” Saboda haka suka fara da dattawan da suke gaban haikali.
7 And he said to them: “Defile the house, and fill its courts with the slain! Go forth!” And they went forth and struck down those who were in the city.
Sa’an nan ya ce musu, “Ku ƙazantar da haikalin ku kuma cika filayen da kisassu. Ku tafi!” Saboda haka suka fita suka kuma fara kisa a duk birnin.
8 And when the slaughter was completed, I remained. And I fell upon my face, and crying out, I said: “Alas, alas, alas, O Lord God! Will you now destroy the entire remnant of Israel, by pouring out your fury upon Jerusalem?”
Yayinda suke kisan sai aka bar ni kaɗai, na fāɗi rubda ciki, na yi kuka na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka dukan raguwar Isra’ila a wannan zafin fushinka a Urushalima?”
9 And he said to me: “The iniquity of the house of Israel, and of Judah, is vast and exceedingly great, and the land has been filled with blood, and the city has been filled with what is abhorrent. For they have said: ‘The Lord has forsaken the earth,’ and, ‘The Lord does not see.’
Ya amsa mini ya ce, “Zunubin gidan Isra’ila da Yahuda ya yi girma ainun; ƙasar ta cika da rashin adalci. Suna cewa, ‘Ubangiji ya yashe ƙasar; Ubangiji ba ya gani.’
10 Therefore, my eye will not be lenient, and I will not take pity. I will repay their own way upon their head.”
Saboda haka ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba, amma zan kawo wa kansu abin da suka yi.”
11 And behold, the man who was clothed with linen, who had a writing instrument at his back, responded a word, saying: “I have done just as you instructed me.”
Sai mutumin da yana saye da lilin yake kuma rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa ya mayar da magana, yana cewa, “Na yi yadda ka umarci ni.”

< Ezekiel 9 >