< Ezekiel 5 >

1 “And as for you, son of man, obtain for yourself a sharp knife for shaving hair, and you shall take it and draw it across your head and across your beard. And you shall obtain for yourself a balance for weighing, and you shall divide the hair.
“Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi ka kuma yi amfani da shi kamar rezan mai aski don askin kanka da gemunka. Sa’an nan ka ɗauki ma’auni ka kuma raba gashin.
2 A third part you shall burn with fire in the midst of the city, according to the completion of the days of the siege. And you shall take a third part, and you shall cut it with the knife all around. Yet truly, the other third, you shall scatter to the wind, for I will unsheathe the sword after them.
Sa’ad da kwanakin ƙawanyarka sun ƙare, sai ka ƙone kashi ɗaya bisa uku na gashin da wuta a cikin birnin. Ka ɗauki kashi ɗaya bisa uku ka yayyanka shi da takobi kewaye da birnin. Ka kuma watsar da kashi ɗaya bisa uku a iska. Gama zan fafare su da takobin da aka zāre.
3 And you shall take from there a small number. And you shall bind them in the end of your cloak.
Amma ka ɗibi gashi kaɗan ka daure a shafin rigarka.
4 And again, you shall take from them, and you shall throw them into the midst of the fire, and you shall burn them with fire. And from it, there shall go forth a fire to the entire house of Israel.”
Har yanzu, ka ɗibi kaɗan na waɗannan ka zuba su cikin wuta su kuma ƙone. Wuta zai bazu daga nan zuwa dukan gidan Isra’ila.
5 Thus says the Lord God: “This is Jerusalem. I have placed her in the midst of the Gentiles and of the lands all around her.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Urushalima ce wannan, wadda na kafa a tsakiyar al’ummai, da ƙasashe kewaye da ita a ko’ina.
6 And she has despised my judgments, so as to be more impious than the Gentiles, and my precepts, more so than the lands that are all around her. For they have cast aside my judgments, and they have not walked in my precepts.”
Duk da haka cikin muguntarta ta yi tayarwa a kan dokokina da ƙa’idodina fiye da al’ummai da ƙasashe kewaye da ita. Ta ƙi dokokina ba tă kuwa bi ƙa’idodina ba.
7 For this reason, thus says the Lord God: “Since you have surpassed the Gentiles who are all around you, and have not walked in my precepts, and have not accomplished my judgments, and have not even acted in accord with the judgments of the Gentiles who are all around you:
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce kin yi ƙin ji fiye da al’umman da suke kewaye da ke ba ki kuma bi ƙa’idodina ko ki kiyaye dokokina ba. Ba ki ma dace da matsayin al’umman da suke kewaye da ke ba.
8 therefore, thus says the Lord God: Behold, I am against you, and I myself will accomplish judgments in your midst, in the sight of the Gentiles.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Ni kaina ina gāba da ke, Urushalima, kuma zan hukunta ki a gaban al’ummai.
9 And I will do in you what I have not done before, and the likes of which I will not do again, because of all your abominations.
Saboda dukan gumakan banƙyamarki, zan yi abin da ban taɓa yi ba, ba kuwa zan ƙara yinsa ba.
10 Therefore, the fathers shall consume the sons in your midst, and the sons shall consume their fathers. And I will execute judgments in you, and I will winnow your entire remnant in every wind.
Saboda haka a cikinki ubanni za su ci’ya’yansu,’ya’ya kuma za su ci ubanninsu. Zan hukunta ki zan kuma watsar da dukan waɗanda suke tsira da suke naki a iska.
11 Therefore, as I myself live says the Lord God, because you have violated my sanctuary with all your offenses and with all your abominations, I also will break into pieces, and my eye will not be lenient, and I will not take pity.
Saboda haka muddin ina a raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin kin ƙazantar da wuri mai tsarkina da dukan mugayen siffofinki da kuma ayyukanki masu banƙyama, ni kaina zan janye alherina; ba zan ji tausayinki ko in haƙura da ke ba.
12 One third part of you will die by pestilence or be consumed by famine in your midst. And one third part of you will fall by the sword all around you. Yet truly, one third part of you I will scatter to every wind, and I will unsheathe the sword after them.
Kashi ɗaya bisa uku na mutanenki za su mutu da annoba ko su mutu da yunwa a cikinki; kashi ɗaya bisa uku takobi ne zai kashe su a waje da katangarki; kashi ɗaya bisa uku kuma zan watsar a iska in kuma fafare su da takobin da aka zāre.
13 And I will fulfill my fury, and I will cause my indignation to rest upon them, and I will be consoled. And they shall know that I, the Lord, have spoken in my zeal, when I will have fulfilled my indignation in them.
“Sa’an nan ne fushina zai huce hasalata a kanki kuma ta lafa, in kuma wartsake. Kuma sa’ad da na zuba fushina a kansu, a sa’an nan ne za su san cewa Ni Ubangiji na yi magana a cikin fushin kishina a kansu.
14 And I will make you desolate, and a disgrace among the Gentiles, who are all around you, in the sight of all who pass by.
“Zan mai da ki kufai da kuma abin dariya a cikin al’ummai kewaye da ke, a gaban dukan waɗanda suke wucewa.
15 And you shall be a disgrace and a blasphemy, an example and an astonishment, among the Gentiles, who are all around you, when I will have executed judgments in you, in fury and in indignation and with rebukes of wrath.
Za ki zama abin dariya da abin ba’a, kashedi da abin banrazana ga al’ummai kewaye da ke sa’ad da na hukunta ki cikin fushi da cikin hasala da kuma tsawatawa mai zafi. Ni Ubangiji na faɗa.
16 I, the Lord, have spoken. At that time, I will send among them the most grievous arrows of famine, which shall bring death, and which I will send so that I may destroy you. And I will gather a famine over you, and I will crush the staff of bread among you.
Sa’ad da na harbe ki da mugayen kibiyoyina da kuma kibiyoyi masu hallakarwa na yunwa, zan yi harbi don in kashe ki. Zan kawo ƙarin yunwa a kanki in kuma yanke tanadin abincinki.
17 And I will send among you famine and very harmful beasts, even unto utter ruin. And pestilence and blood shall pass through you. And I will bring the sword over you. I, the Lord, have spoken.”
Zan aika da yunwa da namun jeji a kanki, za su kuma bar ku ba’ya’ya. Annoba da zub da jini za su ratsa cikinki, zan kuma kawo takobi a kanki. Ni Ubangiji na faɗa.”

< Ezekiel 5 >