< Ezekiel 3 >

1 And he said to me: “Son of man, eat whatever you will find; eat this scroll, and, going forth, speak to the sons of Israel.”
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ci abin da yake a gabanka, ka ci wannan littafi; sa’an nan ka tafi ka yi magana wa gidan Isra’ila.”
2 And I opened my mouth, and he fed me that scroll.
Saboda haka na buɗe bakina, ya kuma ba ni littafin in ci.
3 And he said to me: “Son of man, your stomach shall eat, and your interior shall be filled with this scroll, which I am giving to you.” And I ate it, and in my mouth it became as sweet as honey.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ci wannan littafin da nake ba ka, ka kuma cika cikinka da shi.” Sai na ci shi, ya kuma yi zaki kamar zuma a bakina.
4 And he said to me: “Son of man, go to the house of Israel, and you shall speak my words to them.
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka tafi gidan Isra’ila ka faɗa kalmomina gare su.
5 For you will be sent, not to a people of profound words or of an unknown language, but to the house of Israel,
Ba ina aikan ka wurin mutanen da suke da baƙon harshe da kuma yare mai wuya ba ne, amma zuwa ga gidan Isra’ila ne,
6 and not to many peoples of profound words or of an unknown language, whose words you would not be able to understand. But if you were sent to them, they would listen to you.
ba ga mutane da yawa na baƙon harshe da yare mai wuya, waɗanda ba ka san kalmominsu ba. Tabbatacce da na aike ka wurin irinsu, da sun saurare ka.
7 Yet the house of Israel is not willing to listen to you. For they are not willing to listen to me. Certainly, the entire house of Israel has a brazen forehead and a hardened heart.
Amma gidan Isra’ila ba sa niyya su saurare ka domin ba sa niyya su saurare ni, gama dukan gidan Isra’ila sun taurare suna kuma kin ji.
8 Behold, I have made your face stronger than their faces, and your forehead harder than their foreheads.
Amma zan sa ka zama mai taurinkai da taurin zuciya kamar su.
9 I have made your face like hardened iron and like flint. You should not fear them, and you should not have dread before their face. For they are a provoking house.”
Zan sa goshinka ya zama da tauri kamar dutse, da tauri fiye da dutsen ƙanƙara ƙarfi. Kada ka ji tsoronsu ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.”
10 And he said to me: “Son of man, listen with your ears, and take into your heart, all my words, which I am speaking to you.
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ji da kyau ka kuma lura da dukan kalmomin da nake maka magana.
11 And go forth and enter to those of the transmigration, to the sons of your people. And you shall speak to them. And you shall say to them: ‘Thus says the Lord God.’ Perhaps it may be that they will listen and be quieted.”
Ka tafi yanzu zuwa ga’yan’uwanka waɗanda suke zaman bauta ka yi musu magana. Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa,’ ko ku ji, ko kada ku ji.”
12 And the Spirit took me up, and I heard behind me the voice of a great commotion, saying, “Blessed is the glory of the Lord from his place,”
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama, a bayana na ji wata karar babban motsi na cewa, Bari a yabi ɗaukakar Ubangiji a wurin zamansa!
13 and the voice of the wings of the living creatures striking against one another, and the voice of the wheels following the living creatures, and the voice of a great commotion.
Karar fikafikan rayayyun halittun nan ne suke goge junansu da kuma karar da’irorin nan da suke kusa da su, ƙarar babban motsi.
14 Then the Spirit lifted me and took me away. And I went forth in bitterness, with the indignation of my spirit. For the hand of the Lord was with me, strengthening me.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma tafi da ni, na kuwa tafi da ɓacin rai da kuma fushin ruhuna, tare da hannu mai ƙarfi na Ubangiji a bisa na.
15 And I went to those of the transmigration, to the stockpile of new crops, to those who were living beside the river Chebar. And I sat where they were sitting. And I remained there for seven days, while mourning in their midst.
Na zo wurin masu zaman bautan da suke zama a Tel Abib kusa da Kogin Kebar, A can kuwa, inda suke zama, na zauna a cikinsu kwana bakwai, ina mamaki.
16 Then, when seven days had passed, the word of the Lord came to me, saying:
A ƙarshen kwana bakwai ɗin maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
17 “Son of man, I have made you a watchman for the house of Israel. And so, you shall listen to the word from my mouth, and you shall announce it to them from me.
“Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro don gidan Isra’ila; saboda haka ka ji maganar da zan yi ka kuma yi musu kashedin nan da ya fito daga gare ni.
18 If, when I say to the impious man, ‘You shall certainly die,’ you do not announce it to him, and you do not speak so that he may turn aside from his impious way and live, then the same impious man will die in his iniquity. But I will attribute his blood to your hand.
In na ce wa mugu, ‘Lalle za ka mutu,’ ba ka kuwa yi masa kashedi ko ka tsawata masa a kan mugayen hanyoyinsa don yă ceci ransa ba, wannan mugun zai mutu saboda zunubinsa, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
19 But if you announce it to the impious man, and he is not converted from his impiety and from his impious way, then indeed he will die in his iniquity. But you will have delivered your own soul.
Amma in ka yi wa mugun kashedi bai kuwa juya daga mugayen hanyoyinsa ba, zai mutu saboda zunubinsa; amma kai kam za ka kuɓuta.
20 Moreover, if the just man turns aside from his justice and commits iniquity, I will place a stumbling block before him. He shall die, because you have not announced to him. He shall die in his sin, and his justices that he did shall not be remembered. Yet truly, I will attribute his blood to your hand.
“Har yanzu, in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya aikata mugunta, na kuma sa abin tuntuɓe a gabansa, zai mutu. Da yake ba ka yi masa kashedi ba, zai mutu saboda zunubinsa. Ba za a tuna da abin adalcin da ya yi ba, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
21 But if you announce to the just man, so that the just man may not sin, and he does not sin, then he shall certainly live, because you have announced to him. And you will have delivered your own soul.”
Amma in ka yi wa mai adalcin kashedi kada yă yi zunubi bai kuwa yi zunubi ba, tabbatacce zai rayu saboda ya ji kashedin, kuma kai kam za ka kuɓuta.”
22 And the hand of the Lord was over me. And he said to me: “Rise up, and go out to the plain, and there I will speak with you.”
Hannun Ubangiji ya kasance a kaina a can, ya kuma ce mini, “Tashi ka fita zuwa fili, a can kuwa zan yi maka magana.”
23 And I rose up, and I went out to the plain. And behold, the glory of the Lord was standing there, like the glory that I saw beside the river Chebar. And I fell upon my face.
Saboda haka na tashi da tafi fili. Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta tsaya a can, kamar ɗaukakar da na gani kusa da Kogin Kebar, sai na fāɗi rubda ciki.
24 And the Spirit entered into me, and set me upon my feet. And he spoke to me, and he said to me: “Enter and enclose yourself in the midst of your house.
Sai Ruhu ya sauko a kaina ya kuma ɗaga ni na tsaya a ƙafafuna. Ya yi mini magana ya ce, “Ka fita, ka rufe kanka a cikin gida.
25 And as for you, son of man, behold: they shall put chains upon you and bind you with them. And you shall not go out from their midst.
Kuma kai, ɗan mutum, za su ɗaura ka da igiyoyi; za a daure ka yadda ba za ka iya fita a cikin mutane ba.
26 And I will cause your tongue to adhere to the roof of your mouth. And you will be mute, not like a man who reproaches. For they are a provoking house.
Zan sa harshenka ya manne wa dasashinka don ka yi shiru ka kuma kāsa tsawata musu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
27 But when I will speak to you, I will open your mouth, and you shall say to them: ‘Thus says the Lord God.’ Whoever is listening, let him hear. And whoever is quieted, let him be quieted. For they are a provoking house.”
Amma sa’ad da na yi maka magana, zan buɗe bakinka za ka kuwa faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’ Duk mai ji ya ji, kuma duk wanda ya ƙi ji, ya ƙi ji; gama su gida ne na’yan tawaye.

< Ezekiel 3 >