< Ezekiel 29 >

1 In the tenth year, in the tenth month, on the eleventh day of the month, the word of the Lord came to me, saying:
A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, set your face against Pharaoh, the king of Egypt, and you shall prophesy about him and about all of Egypt.
“Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
3 Speak, and you shall say: Thus says the Lord God: Behold, I am against you, Pharaoh, king of Egypt, you great dragon, who rests in the midst of your rivers. And you say: ‘Mine is the river, and I have made myself.’
Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
4 But I will place a bridle in your jaws. And I will adhere the fish of your rivers to your scales. And I will draw you out of the midst of your rivers, and all your fish will adhere to your scales.
Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
5 And I will cast you into the desert, with all the fish of your river. You will fall upon the surface of the earth; you will not be taken up, nor gathered together. I have given you to the beasts of the earth and to the birds of the air, to be devoured.
Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
6 And all the inhabitants of Egypt shall know that I am the Lord. For you have been a staff made of reed to the house of Israel.
Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
7 When they took hold of you with the hand, you broke, and so you wounded all of their shoulders. And when they leaned on you, you shattered, and so you injured all of their lower backs.
Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
8 Because of this, thus says the Lord God: Behold, I will lead the sword over you, and I will destroy both man and beast from among you.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
9 And the land of Egypt will be a desert and a wilderness. And they shall know that I am the Lord. For you have said, ‘The river is mine, and I have made it.’
Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
10 Therefore, behold, I am against you and against your rivers. And I will make the land of Egypt into a wilderness, destroyed by the sword from the tower of Syene all the way to the borders of Ethiopia.
saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
11 The foot of man will not pass through it, and the foot of cattle will not walk in it. And it will be uninhabited for forty years.
Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
12 And I will set the land of Egypt in desolation, in the midst of desolate lands, and its cities in the midst of overturned cites. And they will be desolate for forty years. And I will scatter the Egyptians among the nations, and I will disperse them among the lands.
Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
13 For thus says the Lord God: After the end of forty years, I will gather the Egyptians from the peoples among whom they had been scattered.
“‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
14 And I will lead back the captivity of Egypt, and I will collect them in the land of Pathros, in the land of their nativity. And in that place, they will be a lowly kingdom.
Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
15 It will be the lowest among the other kingdoms, and it will no longer be exalted above the nations. And I will diminish them, lest they rule over the Gentiles.
Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
16 And they will no longer be the confidence of the house of Israel, teaching iniquity, so that they may flee and follow them. And they shall know that I am the Lord God.”
Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
17 And it happened that, in the twenty-seventh year, in the first month, on the first of the month, the word of the Lord came to me, saying:
A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 “Son of man, Nebuchadnezzar, the king of Babylon, has caused his army to serve with great servility against Tyre. Every head was shaven, and every shoulder was stripped of hair. And wages have not been paid to him, nor to his army, for Tyre, for the service by which he served for me against it.
“Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
19 Because of this, thus says the Lord God: Behold, I will station Nebuchadnezzar, the king of Babylon, in the land of Egypt. And he will take its multitude, and he will prey upon its profits, and he will plunder its spoils. And this shall be the wages for his army
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
20 and for the work by which he has served against it. I have given to him the land of Egypt, because he has labored for me, says the Lord God.
Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 In that day, a horn will spring forth for the house of Israel, and I will give to you an open mouth in their midst. And they shall know that I am the Lord.”
“A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ezekiel 29 >