< Ezekiel 28 >

1 And the word of the Lord came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, say to the leader of Tyre: Thus says the Lord God: Because your heart has been exalted, and you have said, ‘I am God, and I sit in the chair of God, in the heart of the sea,’ though you are a man, and not God, and because you have presented your heart as if it were the heart of God:
“Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
3 Behold, you are wiser than Daniel; no secret is concealed from you.
Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
4 By your wisdom and prudence, you have made yourself strong, and you have acquired gold and silver for your storehouses.
Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
5 By the multitude of your wisdom, and by your business dealings, you have multiplied strength for yourself. And your heart has been exalted by your strength.
Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
6 Therefore, thus says the Lord God: Because your heart has been exalted as if it were the heart of God,
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
7 for this reason, behold, I will lead over you foreigners, the most robust among the Gentiles. And they will bare their swords over the beauty of your wisdom, and they will defile your beauty.
zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
8 They will destroy you and pull you down. And you will die the death of those slain in the heart of the sea.
Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
9 So then, will you speak, in the presence of those who are destroying you, before the hand of those who are killing you, saying, ‘I am God,’ though you are a man, and not God?
Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
10 You will die the death of the uncircumcised at the hand of foreigners. For I have spoken, says the Lord God.”
Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
11 And the word of the Lord came to me, saying: “Son of man, take up a lamentation over the king of Tyre,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
12 and you shall say to him: Thus says the Lord God: You were the seal of similitudes, full of wisdom and perfect in beauty.
“Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
13 You were with the delights of the Paradise of God. Every precious stone was your covering: sardius, topaz, and jasper, chrysolite, and onyx, and beryl, sapphire, and garnet, and emerald. The work of your beauty was of gold, and your fissures were ready in the day when you were formed.
Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
14 You were a cherub, stretched out and protecting, and I stationed you on the holy mountain of God. You have walked in the midst of stones containing fire.
An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
15 You were perfect in your ways, from the day of your formation, until iniquity was found in you.
Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
16 By the multitude of your business dealings, your interior was filled with iniquity, and you sinned. And I cast you away from the mountain of God, and I perished you, O protecting cherub, from the midst of the stones containing fire.
Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
17 And your heart was exalted by your beauty; you have destroyed your own wisdom by your beauty. I have cast you to the ground. I have presented you before the face of kings, so that they may examine you.
Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
18 You have defiled your sanctuaries, by the multitude of your iniquities and by the iniquity of your business dealings. Therefore, I will produce a fire from your midst, which will consume you, and I will make you into ashes upon the earth, in the sight of all who are watching you.
Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
19 All who gaze upon you among the Gentiles will be stupefied over you. You were made out of nothing, and you shall not be, forever.”
Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
20 And the word of the Lord came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
21 “Son of man, set your face against Sidon, and you shall prophesy about it.
“Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
22 And you shall say: Thus says the Lord God: Behold, I am against you, Sidon, and I will be glorified in your midst. And they shall know that I am the Lord, when I will have executed judgments in her, and when I will have been sanctified in her.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
23 And I will send a pestilence upon her, and there will be blood in her streets. And they will fall, slain by the sword, on every side in her midst. And they shall know that I am the Lord.
Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
24 And the house of Israel will no longer be a stumbling block of bitterness, nor a thorn bringing pain everywhere around them, to those who turn against them. And they shall know that I am the Lord God.”
“‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
25 Thus says the Lord God: “When I will have gathered together the house of Israel, from the peoples among whom they have been dispersed, I shall be sanctified in them in the sight of the Gentiles. And they shall live in their own land, which I gave to my servant Jacob.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
26 And they shall live within it securely. And they shall build houses and plant vineyards. And they shall live in confidence, when I will have executed judgments upon all those who turn against them on every side. And they shall know that I am the Lord their God.”
Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”

< Ezekiel 28 >