< Ezekiel 27 >

1 And the word of the Lord came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “You, therefore, son of man, take up a lamentation over Tyre.
“Ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya.
3 And you shall say to Tyre, which lives at the entrance to the sea, which is the marketplace of the peoples for the many islands: Thus says the Lord God: O Tyre, you have said, ‘I am of perfect beauty,
Ka ce wa Taya, wadda take zaune a hanyar shiga zuwa teku, kasuwar masu yawa mutane a bakin teku, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kin ce, ya Taya, “Ni kyakkyawa ce cikakkiya.”
4 for I have been positioned at the heart of the sea!’ Your neighbors, who built you, have filled up your beauty.
Manyan tekuna ne wurin zamanki; maginanki sun sa kyanki ya zama cikakke.
5 They constructed you with spruce from Senir, with all the planks of the sea. They have taken cedars from Lebanon, so that they might make a mast for you.
Sun yi dukan katakanki daga itatuwan fir daga Senir; sun kwaso itatuwan al’ul daga Lebanon don su yi miki jigon jirgin ruwa.
6 They have formed your oars from the oaks of Bashan. And they have made your crossbeams from Indian ivory, and the pilothouse is from the islands of Italy.
Da oak daga Bashan suka yi sandunan tuƙan jirgin ruwa da itatuwan kasharina daga bakin tekun Saifurus suka yi daɓe jirgin ruwanki, suka kuma manne masa hauren giwa.
7 Colorful fine linen from Egypt was woven for you as a sail to be placed upon the mast; hyacinth and purple from the islands of Elishah were made into your covering.
Lilin mai kyau mai ado daga Masar ne filafilan jirgin ruwanki suka kuma zama tutarki; an yi tutarki da shuɗi da shunayya daga bakin tekun Elisha.
8 The inhabitants of Sidon and of Arwad were your rowers. Your wise ones, O Tyre, were your navigators.
Mutanen Sidon da Arfad su ne matuƙan jirgin ruwanki; gwanayenki, ya Taya, suna ciki a matsayi matuƙan jiragen ruwa.
9 The elders of Gebal and its experts were considered as sailors making use of your diverse equipment. All the ships of the sea and their sailors were your merchants among the people.
Masu hikima na Gebal suna ciki a matsayin masu tattoshe mahaɗan katakon jirginki. Dukan jiragen ruwa da matuƙansu sukan zo wurinki don kasuwanci.
10 The Persians, and the Lydians, and the Libyans were your men of war in your army. They suspended shield and helmet within you for your adornment.
“‘Mutanen Farisa, Lidiya da Fut su ne suka zama sojoji a cikin mayaƙanki. Sun rataye garkuwoyinsu da hulunan kwano a katangarki, suna kawo miki daraja.
11 The sons of Arwad were with your army upon your walls all around. And even the Gammadim, who were in your towers, suspended their quivers on your walls on all sides; they completed your beauty.
Mutanen Arfad da Helek sun yi tsaron katangar a kowace gefe; mutanen Gammad su ne a hasumiyoyinki. Sun rataye garkuwoyinsu kewaye da katangarki; sun sa kyanki ya zama cikakke.
12 The Carthaginians, your merchants, supplied your festivals with a multitude of diverse riches, with silver, iron, tin, and lead.
“‘Tarshish ta yi ciniki da ke saboda yawan wadatar kayayyakinki; sun sayi kayan cinikinki da azurfa, ƙarfe, kuza da dalma.
13 Greece, Tubal, and Meshech, these were your peddlers; they traveled to your people with slaves and with brass vessels.
“‘Girka, Tubal da Meshek sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki suka biya da bayi da kuma abubuwan da aka yi da tagulla.
14 From the house of Togarmah, they brought horses, and horsemen, and mules to your market.
“‘Mutanen Bet Togarma sun sayi kayan cinikinki da dawakai, dawakan yaƙi da alfadarai.
15 The sons of Dedan were your merchants. The many islands were the marketplace of your hand. They traded teeth of ivory and of ebony for your price.
“‘Mutanen Dedan sun yi kasuwanci da ke, bakin teku masu yawa abokan cinikinki ne; sun biya ki da hauren giwa da katakon kanya.
16 The Syrian was your merchant. Because of the multitude of your works, they offered jewels, and purple, and patterned cloth, and fine linen, and silk, and other valuables in your market.
“‘Mutanen Aram sun yi ciniki da ke saboda yawan kayanki; suka sayi kayan cinikinki da zumurrudu, da shunayya, da kayan ado, da lilin mai taushi, da murjani, da yakutu.
17 Judah and the land of Israel, these were your peddlers of the best grain; they offered balsam, and honey, and oil, and resins at your festivals.
“‘Yahuda da Isra’ila sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki da alkama da Minnit da alawa, da zuma, da mai, da ganyaye masu ƙanshi.
18 The Damascene was your trader in the multitude of your works, in greatly diverse wealth, in rich wine, in wool with the finest coloring.
“‘Mutanen Damaskus sun ga abin da za ki iya bayarwa sai suka yi ciniki da ke, ta sayi kayanki da ruwan inabi daga Helbon, da ulu daga Zahar.
19 Dan, and Greece, and Mosel have offered works made of iron at your festivals. Storax ointment and sweet flag were in your marketplace.
Wedan da Yaban kusa da Uzal, suka sayi kayanki; wato gyararren ƙarfe da kayan yaji.
20 The men of Dedan were your peddlers of tapestries used as seats.
“‘Mutanen Dedan sun sayi kayanki da sirdin zama a kan dawakai.
21 Arabia and all the leaders of Kedar, these were the merchants at your hand. Your merchants came to you with lambs, and rams, and young goats.
“‘Mutanen Arabiya da dukan sarakunan Kedar abokan cinikinki ne; sun yi ciniki da ke suka sayi kayanki da’yan raguna, da raguna, da awaki.
22 The vendors of Sheba and Raamah, these were your merchants, with all the finest aromatics, and precious stones, and gold, which they offered in your marketplace.
“‘’Yan kasuwan Sheba da Ra’ama sun yi ciniki da ke; suka sayi kayanki da kayan yaji mafi kyau iri-iri, da duwatsu masu daraja iri-iri, da zinariya.
23 Haran, and Canneh, and Eden were your merchants. Sheba, Assur, and Chilmad were your sellers.
“‘Haran, Kanne da Eden da kuma’yan kasuwan Sheba, Assuriya da Kilmad sun yi ciniki da ke.
24 These were your merchants in many places, with windings of hyacinth and of colorful weavings, and with precious treasures, which were wrapped and bound with cords. Also, they had works of cedar among your merchandise.
A kasuwarki sun yi ciniki da ke suka sayar miki tufafi masu tsada, da na shuɗi, da masu ado, da dardumai masu ƙyalƙyali da kirtani, da igiyoyi waɗanda aka tuƙa da kyau.
25 The ships of the sea were important to your business dealings. For you were replenished and exceedingly glorified in the heart of the sea.
“‘Jiragen ruwan Tarshish sun zama masu jigilar kayanki. Kin cika da kaya masu nauyi a tsakiyar teku.
26 Your rowers have brought you into many waters. The south wind has worn you down in the heart of the sea.
Matuƙan jiragenki sun kai ki can cikin manyan tekuna. Amma iskar gabas za tă farfasa ki kucu-kucu a tsakiyar teku.
27 Your riches, and your treasures, and your versatile equipment, your sailors and your navigators, who handle your goods and who were first among your people, likewise your men of war, who were among you, and your entire multitude that is in your midst: they will fall in the heart of the sea on the day of your ruin.
Dukiyarki, cinikinki da kayan kasuwarki, ma’aikatanki na jirgi, matuƙan jiragenki da masu tattoshe mahaɗan katakan jiragenki,’yan kasuwarki da dukan sojojinki, da kuma kowa da yake cikin jirgi zai nutsa a tsakiyar teku a ranar da jirginki zai nutse.
28 Your fleets will be disturbed by the sound of an outcry from your navigators.
Ƙasashen bakin teku za su girgiza sa’ad da matuƙan jirginki suka yi kuka.
29 And all who were handling the oar will descend from their ships; the sailors and all the navigators of the sea will stand upon the land.
Dukan waɗanda suke riƙe da matuƙi za su ƙyale jiragensu; ma’aikatan jirage da dukan matuƙan jirage za su tsaya a bakin teku.
30 And they will howl over you with a great voice, and they will cry out with bitterness. And they will cast dust upon their heads, and they will be sprinkled with ashes.
Za su tā da muryarsu su yi kuka mai zafi a kanki; za su yayyafa ƙura a kawunansu, su yi ta birgima a cikin toka.
31 And they will shave their heads because of you, and they will be wrapped in haircloth. And they will weep for you with bitterness of soul, with a very bitter weeping.
Za su aske kawunansu saboda ke za su kuma sa tufafin makoki. Za su yi kuka dominki su yi ɓacin rai da kuma kuka mai zafi.
32 And they will take up a mournful verse over you, and they will lament you: ‘What city is like Tyre, which has become mute in the midst of the sea?’
Yayinda suke kuka a kanki kuwa, za su yi makoki dominki suna cewa, “Wa ya taɓa yin shiru kamar Taya, kewaye da teku?”
33 For by the going forth of your merchandise by sea, you supplied many peoples; by the multitude of your riches and of your people, you enriched the kings of the earth.
Sa’ad da kayan cinikinki suka tafi ƙasashen hayi, kin gamsar da al’ummai masu yawa; da dukiyarki masu yawa da kuma kayan cinikinki kin azurtar da sarakunan duniya.
34 Now you have been worn away by the sea, your opulence is in the depths of the waters, and your entire multitude that was in your midst has fallen.
Yanzu teku ta farfashe ki cikin zurfafan ruwaye; kayan cinikinki da dukan kamfaninki sun nutse tare da ke.
35 All the inhabitants of the islands have been stupefied over you; and all their kings, having been struck by the tempest, have changed their expression.
Dukan mazaunan bakin teku sun giggice saboda masifarki; sarakunansu sun tsorata ƙwarai fuskokinsu kuwa sun yamutse don tsoro.
36 The merchants of the peoples have hissed over you. You have been reduced to nothing, and you shall not be again, even forever.”
’Yan kasuwa a cikin al’ummai suna yin miki tsaki; kin zo ga mummunar ƙarshe ba za ki ƙara kasancewa ba har abada.’”

< Ezekiel 27 >