< Ezekiel 26 >

1 And it happened that, in the eleventh year, on the first of the month, the word of the Lord came to me, saying:
A shekara ta goma sha ɗaya, a rana ta fari ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, because Tyre has said about Jerusalem: ‘It is Well! The gates of the peoples have been broken! She has been turned toward me. I will be filled. She will be deserted!’
“Ɗan mutum, domin Taya ta yi magana a kan Urushalima ta ce, ‘Yauwa! Ƙofar zuwa al’ummai ta karye, an kuma buɗe mini ƙofofinta; yanzu da take kufai zan wadace,’
3 because of this, thus says the Lord God: Behold, I am against you, O Tyre, and I will cause many nations to rise up against you, just as the waves of the sea rise up.
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da ke, ya Taya, zan kuwa kawo al’ummai masu yawa su yi gāba da ke, kamar yadda teku takan kawo raƙuman ruwa.
4 And they will break apart the walls of Tyre, and they will destroy its towers. And I will scrape her dust from her, and I will make her into the barest rock.
Za su hallaka katangar Taya su kuma rurrushe hasumiyoyinta; zan kankare tarkacenta, in maishe ta fā.
5 She will be a drying place for nets from the midst of the sea. For I have spoken, says the Lord God. And she will be a spoil for the Gentiles.
Za tă zama wurin shanya abin kamun kifi a tsakiyar teku, gama na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Za tă zama ganima ga sauran al’ummai,
6 Likewise, her daughters who are in the field will be slain by the sword. And they shall know that I am the Lord.
za a kashe mazaunan filin ƙasar da takobi. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.
7 For thus says the Lord God: Behold, I will lead into Tyre: Nebuchadnezzar, the king of Babylon, a king among kings, from the north, with horses, and chariots, and horsemen, and companies, and a great people.
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa daga arewa zan kawo wa Taya Nebukadnezzar sarkin Babilon, sarkin sarakuna, tare da dawakai da kekunan yaƙi, da mahayan dawakai da babbar rundunar soja.
8 Your daughters who are in the field, he will kill with the sword. And he will surround you with fortifications, and he will put together a rampart on all sides. And he will lift up a shield against you.
Zai kashe mazaunan filin ƙasar da takobi; zai yi miki ƙawanya, ya gina miki mahaurai, sa’an nan ya rufe ki da garkuwoyi.
9 And he will combine moveable shelters and battering rams before your walls, and he will destroy your towers with his armaments.
Zai rushe katangarki da dundurusai, ya rurrushe hasumiyoyinki da makamai.
10 He will cover you with the inundation of his horses and with their dust. Your walls will shake at the sound of horsemen and wheels and chariots, when they will have entered your gates, as if through the entrance of a city that has been broken open.
Dawakansa za su yi yawa har su rufe ke da ƙura. Katanga za su girgiza saboda motsin dawakan yaƙi, kekunan doki da keken yaƙin sa’ad da suka shiga birnin da aka rushe katangar.
11 With the hoofs of his horses, he will trample all your streets. He will cut down your people with the sword, and your noble statues will fall to the ground.
Kofatan dawakansa za su tattake dukan titunanki; zai kashe mutanenki da takobi, ginshiƙanki masu ƙarfi kuma za su fāɗi a ƙasa.
12 They will lay waste to your wealth. They will despoil your businesses. And they will tear down your walls and overturn your eminent houses. And they will put your stones and your timber and your dust into the midst of the waters.
Za su washe dukiyarki, kayan cinikinki kuma su zama ganima; za su rurrushe katangarki su ragargaza gidajenki masu kyau su kuma zubar da duwatsunki, katakanki da kuma tarkacenki a cikin teku.
13 And I will cause the multitude of your songs to cease. And the sound of your stringed instruments will no longer be heard.
Zan kawo ƙarshen waƙoƙinki masu surutu, ba kuwa za a ƙara jin kaɗe-kaɗen garayunki ba.
14 And I will make you like the barest rock; you will be a drying place for nets. And you will no longer be built up. For I have spoken, says the Lord God.”
Zan maishe ki fā, za ki kuma zama wurin shanya abin kamun kifi. Ba za a sāke gina ki ba, gama Ni Ubangiji na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Thus says the Lord God to Tyre: “Will not the islands shake at the sound of your ruin and at the groans of your slain, when they will have been cut down in your midst?
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Taya. Ƙasashen da suke a bakin teku ba za su girgiza saboda ƙarar fāɗuwarki, sa’ad da nishin waɗanda aka yi wa rauni da kashe-kashen da aka yi a cikinki suka faru ba?
16 And all the leaders of the sea will descend from their thrones. And they will cast aside their outer garments and their colorful clothing, and they will be clothed in stupor. They will sit on the ground, and they will wonder with astonishment at your sudden downfall.
Sa’an nan sarakunan bakin teku za su sauka daga gadajen sarautarsu, su tuɓe rigunansu, da rigunansu waɗanda aka yi wa ado. Za su zauna a ƙasa suna rawar jiki a kowane lokaci suna razana saboda abin da ya same ki.
17 And taking up a lamentation over you, they will say to you: ‘How could you have perished, you who live in the sea, the famous city that was strong in the sea, with your inhabitants, of whom the whole world was in dread?’
Sa’an nan za su yi makoki game da ke su ce, “‘Yaya kika hallaka haka nan, ya birnin da ta yi suna, cike da mutanen teku! Ke da kika zama mai ƙarfi cikin tekuna, ke da mazauna cikinki; kin sa tsoronki a kan dukan waɗanda suka zauna a can.
18 Now the ships will be stupefied, in the day of your terror. And the islands of the sea will be disturbed, because no one goes out from you.
Yanzu tsibirai suna rawar jiki a ranar fāɗuwarki; tsibirai a cikin teku sun tsorata a ɓacewarki.’
19 For thus says the Lord God: When I will have made you a desolate city, like the cities that are uninhabited, and when I will have led the abyss over you, and many waters will have covered you,
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na maishe ki kufai, kamar sauran biranen da ba a ƙara zama a ciki, sa’ad da kuma na kawo zurfafan teku a kanki da yawan ruwansa suka rufe ki,
20 and when I will have dragged you down with those who descend into the pit to the everlasting people, and when I will have assembled you in the lowest parts of the earth, like the desolate places of antiquity, with those who have been brought down into the pit, so that you will be uninhabited, and moreover, when I will have given glory to the land of the living:
a sa’an nan zan sauko da ke ƙasa tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, zuwa wurin mutanen dā. Zan sa ki zauna ƙarƙashin ƙasa, kamar a kufai na tun dā, tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, ba kuwa za ki ƙara dawowa ba ko ki ɗauki matsayinki a ƙasar masu rai.
21 I will reduce you to nothing, and you shall not be, and if you are sought, you will no longer be found, in perpetuity, says the Lord God.”
Zan sa ki yi mummunan ƙarshe kuma ba za ki ƙara kasancewa ba. Za a neme ki, amma ba za a ƙara same ki ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 26 >