< Ezekiel 18 >

1 And the word of the Lord came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Why is it that you circulate among yourselves this parable, as a proverb in the land of Israel, saying: ‘The fathers ate a bitter grape, and the teeth of the sons have been affected.’
“Me ku mutane kuke nufi da faɗar wannan karin magana a kan ƙasar Isra’ila cewa, “‘Ubanni sun ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya kuwa sun mutu’?
3 As I live, says the Lord God, this parable shall no longer be a proverb for you in Israel.
“Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba za ku ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.
4 Behold, all souls are mine. Just as the soul of the father is mine, so also is the soul of the son. The soul that sins, the same shall die.
Gama kowane mai rai nawa ne, mahaifi da ɗa, duk nawa ne. Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu.
5 And if a man is just, and he accomplishes judgment and justice,
“A ce akwai mai adalci wanda yake aikata abin da yake daidai da kuma gaskiya;
6 and if he does not eat upon the mountains, nor lift up his eyes to the idols of the house of Israel, and if he has not violated the wife of his neighbor, nor approached a menstruating woman,
ba ya cin abinci a duwatsun tsafi ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Ba ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa ko ya kwana da mace lokacin al’adarta ba.
7 and if he has not grieved any man, but has restored the collateral to the debtor, if he has seized nothing by violence, has given his bread to the hungry, and has covered the naked with a garment,
Ba ya cin zalin wani, amma yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa. Ba ya yi fashi amma yakan ba wa mayunwata abinci ya kuma tanada wa marasa tufafi riga.
8 if he has not lent upon usury, nor taken any increase, if he has averted his hand from iniquity, and has executed true judgment between man and man,
Ba ya ba da bashi da ruwa ko ya karɓa ƙarin riba. Yakan janye hannunsa daga aikata mugunta yakan kuma yi shari’a cikin gaskiya tsakanin mutum da mutum.
9 if he has walked in my precepts and kept my judgments, so that he acts in accord with truth, then he is just; he shall certainly live, says the Lord God.
Yana bin ƙa’idodina yana kuma kiyaye dokokina da aminci. Wannan mutumin adali ne; tabbatacce zai rayu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
10 But if he raises a son who is a robber, who sheds blood, and who does any of these things,
“A ce yana da ɗa wanda yana kisa ko yana yin ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa
11 (even though he himself does not do any of these things, ) and who eats upon the mountains, and who defiles the wife of his neighbor,
(ko da yake mahaifin bai yi ko ɗaya daga cikinsu ba). “Yakan ci abinci a duwatsun tsafi. Yakan ƙazantar da matar maƙwabci.
12 who grieves the needy and the poor, who seizes with violence, who does not restore the collateral, and who lifts up his eyes to idols, committing abomination,
Yakan ci zalin matalauta da mabukata. Yakan yi fashi. Ba ya mayar da abin da aka jinginar masa. Ya dogara ga gumaka. Yana aikata ayyukan banƙyama.
13 who lends upon usury, and who takes an increase, then shall he live? He shall not live. Since he has done all these detestable things, he shall certainly die. His blood shall be upon him.
Yakan ba da bashi da ruwa ya kuma karɓi riba mai yawa. Irin wannan mutum zai rayu? Ba zai rayu ba! Domin ya aikata dukan waɗannan abubuwa masu banƙyama, tabbatacce za a kashe shi, kuma hakkin jininsa zai zauna a kansa.
14 But if he raises a son, who, seeing all his father’s sins that he has done, is afraid and so does not act in a way similar to him,
“Amma a ce wannan ɗa yana da ɗa wanda ya ga dukan zunuban da mahaifinsa yake aikata, kuma ko da yake ya gan su, bai yi ko ɗaya daga cikin irin abubuwan nan ba, wato,
15 who does not eat upon the mountains, nor lift up his eyes to the idols of the house of Israel, and who does not violate the wife of his neighbor,
“Bai ci abinci a duwatsun tsafi ba ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Bai ƙazantar da matar maƙwabcinsa ba.
16 and who has not grieved any man, nor withheld the collateral, nor seized by violence, but instead has given his bread to the hungry, and has covered the naked with a garment,
Bai ci zalin wani ko ya karɓi jingina ba. Ba ya fashi amma yakan ba da abincinsa ga mayunwata ya tanada tufafi wa marasa tufafi.
17 who has averted his hand from injuring the poor, who has not taken usury and an overabundance, who has acted according to my judgments and walked in my precepts, then this one shall not die for the iniquity of his father; instead, he shall certainly live.
Yakan janye hannunsa daga zunubi ba ya kuma ba da bashi da ruwa ko karɓan riba da yawa. Yakan kiyaye dokokina ya kuma bi ƙa’idodina. Ba zai mutu saboda zunubin mahaifinsa ba; tabbatacce zai rayu.
18 As for his father, because he oppressed and did violence to his brother, and worked evil in the midst of his people, behold, he has died by his own iniquity.
Amma mahaifinsa zai mutu saboda zunubinsa, domin ya yi ƙwace, ya yi wa ɗan’uwansa fashi ya kuma yi abin da ba daidai ba a cikin mutanensa.
19 And you say, ‘Why has not the son borne the iniquity of the father?’ Clearly, since the son has worked judgment and justice, has observed all my precepts, and has done them, he shall certainly live.
“Duk da haka kukan yi tambaya, ‘Me ya sa ɗan ba zai sami rabo a laifin mahaifinsa ba?’ Da yake ɗan ya yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina, tabbatacce zai rayu.
20 The soul that sins, the same shall die. The son shall not bear the iniquity of the father, and the father shall not bear the iniquity of the son. The justice of the just man shall be upon himself, but the impiety of the impious man shall be upon himself.
Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu. Ɗa ba zai sami rabo a laifin mahaifi ba, mahaifi ba zai sami rabo a laifi ɗa ba. Adalcin adali zai zama nasa, muguntar mugu za tă koma kansa.
21 But if the impious man does penance for all his sins which he has committed, and if he keeps all my precepts, and accomplishes judgment and justice, then he shall certainly live, and he shall not die.
“Amma in mugun mutum ya juya daga dukan zunubin da ya aikata ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina ya kuwa yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
22 I will not remember all his iniquities, which he has worked; by his justice, which he has worked, he shall live.
Babu laifin da ya yi da za a tuna da su. Saboda abubuwan adalcin da ya aikata, zai rayu.
23 How could it be my will that an impious man should die, says the Lord God, and not that he should be converted from his ways and live?
Ina jin daɗin mutuwar mugu ne? In ji Ubangiji Mai Iko Duka. A maimako, ban fi jin daɗi sa’ad da suka juyo daga hanyoyinsu suka rayu ba?
24 But if a just man turns himself away from his justice, and does iniquity in accord with all the abominations that the impious man so often does, why should he live? All his justices, which he has accomplished, shall not be remembered. By the transgression, in which he has transgressed, and by his sin, in which he has sinned, by these he shall die.
“Amma in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya yi zunubi ya kuma aikata abubuwa masu banƙyamar da mugun mutum ke aikatawa, zai rayu? Babu abubuwan adalcin da ya aikata da za a tuna da su. Saboda rashin amincinsa da kuma saboda zunubai da ya yi, zai mutu.
25 And you have said, ‘The way of the Lord is not fair.’ Therefore, listen, O house of Israel. How could it be that my way is not fair? And is it not instead your ways that are perverse?
“Duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ka ji, ya gidan Isra’ila. Hanyata ba daidai ba ce?
26 For when the just man turns himself away from his justice, and commits iniquity, he shall die by this; by the injustice that he has worked, he shall die.
In mai adalci ya juye daga adalcinsa ya yi zunubi, zai mutu saboda wannan; saboda zunubin da ya yi, zai mutu.
27 And when the impious man turns himself away from his impiety, which he has done, and accomplishes judgment and justice, he shall cause his own soul to live.
Amma in mugun mutum ya juye daga muguntarsa ya kuma yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, zai ceci ransa.
28 For by considering and turning himself away from all his iniquities, which he has worked, he shall certainly live, and he shall not die.
Domin ya lura da dukan laifofin da ya yi ya kuma juye daga gare su, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
29 And yet the sons of Israel say, ‘The way of the Lord is not fair.’ How could it be that my ways are not fair, O house of Israel? And is it not instead your ways that are perverse?
Duk da haka mutanen Isra’ila sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Hanyoyina ba daidai ba ne, ya gidan Isra’ila? Ba hanyoyinku ne ba daidai ba?
30 Therefore, O house of Israel, I will judge each one according to his ways, says the Lord God. Be converted, and do penance for all your iniquities, and then iniquity will not be your ruin.
“Saboda haka, ya gidan Isra’ila, zan hukunta ku, kowa bisa ga hanyarsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba! Ku juye daga dukan laifofinku; sa’an nan zunubi ba zai zama sanadin fāɗuwarku ba.
31 Cast all your transgressions, by which you have transgressed, away from you, and make for yourselves a new heart and a new spirit. And then why should you die, O house of Israel?
Ku raba kanku da dukan laifofin da kuka yi, ku sami sabuwar zuciya da sabon ruhu. Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?
32 For I do not desire the death of one who dies, says the Lord God. So return and live.”
Gama ba na jin daɗin mutuwar wani, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba don ku rayu!

< Ezekiel 18 >