< Ezekiel 13 >

1 And the word of the Lord came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, prophesy to the prophets of Israel who are prophesying, and you shall say to those who prophesy from their own heart: Hear the word of the Lord:
“Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
3 Thus says the Lord God: Woe to the foolish prophets, who are following their own spirit, and who see nothing.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
4 Your prophets, O Israel, were like foxes in the deserts.
Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
5 You have not gone up against the adversary, and you have not established a wall for the house of Israel, so as to stand in battle on the day of the Lord.
Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
6 They see emptiness, and they foretell falsehoods, saying, ‘The Lord says,’ though the Lord has not sent them. And they continued to affirm what they said.
Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
7 Have you not seen a futile vision and spoken a lying divination? And yet you say, ‘The Lord says,’ though I have not spoken.
Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
8 Because of this, thus says the Lord God: Since you have spoken emptiness and have seen falsehoods, therefore: behold, I am against you, says the Lord God.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 And my hand will be over the prophets who are seeing emptiness and divining lies. They shall not be in the council of my people, and they shall not be written in the writing of the house of Israel. Neither shall they enter into the land of Israel. And you shall know that I am the Lord God.
Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
10 For they have deceived my people, saying, ‘Peace,’ and there is no peace. And they have built a wall, but they have covered it in clay without straw.
“‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
11 Say to those who spread mortar without mixing, that it will fall apart. For there will be an inundating rain, and I will cause full-grown hailstones to rush down from above, and a windstorm to dissipate it.
saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
12 So then, behold: when the wall has fallen, will it not be said to you: ‘Where is the mortar with which you covered it?’
Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
13 Because of this, thus says the Lord God: And I will cause a violent wind to burst forth in my indignation, and there will be an inundating rain in my fury, and great hailstones in wrath, to consume.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
14 And I will destroy the wall that you have covered without tempering it. And I will level it to the ground, and its foundation will be revealed. And it will fall and be consumed in its midst. And you shall know that I am the Lord.
Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
15 And I will fulfill my indignation against the wall, and against those who cover it without mixing the mortar, and I will say to you: The wall is no more, and those who covered it are no more:
Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
16 the prophets of Israel, who prophesy to Jerusalem, and who see visions of peace for her when there is no peace, says the Lord God.
waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
17 And as for you, son of man, set your face against the daughters of your people, who prophesy from their own heart. And prophesy about them,
“To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
18 and say: Thus says the Lord God: Woe to those who sew together little pillows under every forearm, and who make little cushions for the heads of every stage of life, in order to capture souls. And when they have seized the souls of my people, they became the life of their souls.
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
19 And they violated me among my people, for the sake of a handful of barley and a fragment of bread, so that they would kill the souls that should not die, and enliven the souls that should not live, lying to my people who believe in falsehoods.
Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
20 Because of this, thus says the Lord God: Behold, I am against your little pillows, with which you catch flying souls. And I will tear them away from your arms. And I will release the souls that you are capturing, the souls that should fly.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
21 And I will tear away your little cushions. And I will free my people from your hand. And they shall no longer be a prey in your hands. And you shall know that I am the Lord.
Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
22 For by deception you have caused the heart of the just to grieve, whom I would not sadden. And I have strengthened the hands of the impious, so that he would not be turned back from his evil way and live.
Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
23 Therefore, you shall not see emptiness, and you shall not divine divinations, any more. And I will rescue my people from your hand. And you shall know that I am the Lord.”
saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”

< Ezekiel 13 >