< Exodus 31 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying:
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Behold, I have called by name Bezalel the son of Uri, the son of Hur, from the tribe of Judah,
“Duba, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuda,
3 and I have filled him with the Spirit of God, with wisdom, and understanding, and knowledge in every craft,
na kuma cika shi da Ruhun Allah, fasaha, azanci, da kuma sani cikin kowace irin sana’a,
4 in order to design whatever must be fabricated from gold, and silver, and brass,
don yin zāne-zāne na aikin zinariya, azurfa da tagulla,
5 from marble, and precious stones, and various woods.
don yanka da shirya duwatsu, yin aikin katako, da kuma yin kowane irin aikin sana’ar hannu.
6 And I have given to him, as his associate, Oholiab the son of Ahisamach, from the tribe of Dan. And I have placed wisdom in the heart of every artisan, so that they may make everything as I have instructed you:
Ban da haka, na zaɓi Oholiyab ɗan Ahisamak, na kabilar Dan, don yă taimake shi. Na kuma ba da fasaha ga dukan masu aikin sana’ar hannu, don yin duk abin da na umarce ka.
7 the tabernacle of the covenant, and the ark of the testimony, and the propitiatory which is over it, and all the vessels of the tabernacle,
Tentin Sujada, akwatin Alkawari tare da murfin kafara a bisansa, da dukan kayan aiki na tentin,
8 and the table and its vessels, the most pure lampstand with its vessels, and the altars of incense
tebur da kayansa, wurin ajiye fitila na zinariya zalla, da dukan kayansa, bagaden ƙona turare,
9 and of holocaust and all their vessels, the washtub with its base,
bagaden hadaya ta ƙonawa da dukan kayansa, daro tare da mazauninsa,
10 the holy vestments for the ministry of Aaron the priest, and for his sons, so that they may execute their office of sacred rites,
da kuma saƙaƙƙun riguna, tsarkakan riguna don Haruna firist da rigunan’ya’yansa maza, sa’ad da suke hidima a matsayin firistoci,
11 the oil of unction, and the incense of aromatics in the Sanctuary. All the things that I have instructed you, they shall make.”
da man shafewa, da turare mai ƙanshi don Wuri Mai Tsarki. Za a yi su kamar yadda na umarce ka.”
12 And the Lord spoke to Moses, saying:
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
13 “Speak to the sons of Israel, and you shall say to them: See that you keep my Sabbath. For it is a sign between me and you among your generations, so that you may know that I am the Lord, who sanctifies you.
“Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Dole ku kiyaye Asabbataina. Wannan zai zama alama tsakanina da ku daga tsara zuwa tsara, saboda ku sani ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.
14 Keep my Sabbath, for it is holy to you. Whoever will have polluted it, shall die a death. Whoever will have done any work in it, his soul shall perish from the midst of his people.
“‘Ku kiyaye Asabbaci, domin yă zama mai tsarki a gare ku. Duk wanda ya ƙazantar da shi, za a kashe shi; duk wanda ya yi wani aiki a ranar, za a ware shi daga mutane.
15 For six days you shall do work. On the seventh day, it is the Sabbath, a rest sanctified by the Lord. All who will have done work on this day shall die.
Kwana shida, za a yi aiki, amma a rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, mai tsarki ga Ubangiji. Duk wanda ya yi wani aiki a Asabbaci, za a kashe shi.
16 Let the sons of Israel keep the Sabbath, and let them celebrate it throughout their generations. It is an everlasting covenant
Isra’ilawa za su kiyaye Asabbaci, suna bikinsa daga tsara zuwa tsara a matsayin madawwamin alkawari.
17 between me and the sons of Israel, and a perpetual sign. For in six days the Lord made heaven and earth, and in the seventh he ceased from work.”
Zai zama alama tsakanina da Isra’ilawa har abada, gama cikin kwana shida Ubangiji ya yi sama da ƙasa, a rana ta bakwai kuma ya daina aiki, ya kuma huta.’”
18 And the Lord, having completed speaking in this way on Mount Sinai, gave to Moses two stone tablets of testimony, written with the finger of God.
Sa’ad da Ubangiji ya gama yin wa Musa magana a kan Dutsen Sinai, sai ya ba shi alluna biyu na Alkawari, allunan duwatsu rubutattu da yatsan Allah.

< Exodus 31 >