< Exodus 10 >

1 And the Lord said to Moses: “Enter to Pharaoh. For I have hardened his heart, and that of his servants, so that I may accomplish these, my signs, in him,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
2 and so that you may describe to the ears of your sons and your grandsons how often I opposed the Egyptians and wrought my signs among them, and so that you may know that I am the Lord.”
don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
3 Therefore, Moses and Aaron entered to Pharaoh, and they said to him: “Thus says the Lord God of the Hebrews: How long will you be unwilling to be subject to me? Release my people to sacrifice to me.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
4 But if you resist, and you are unwilling to release them, behold, tomorrow I will bring locusts into your borders.
In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
5 And they shall cover the face of the earth, lest any part of it be seen. Yes, and what remains from the hail shall be eaten. For they will gnaw away all the trees that spring up in the fields.
Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
6 And they will fill your houses, and those of your servants and of all the Egyptians: so many as your fathers and ancestors have not seen, from the time that they rose up over the earth, even until this present day.” And he turned himself away, and he departed from Pharaoh.
Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
7 Then the servants of Pharaoh said to him: “How long must we endure this scandal? Release the men, in order to sacrifice to the Lord their God. Do you not see that Egypt is perishing?”
Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
8 And they called back Moses and Aaron to Pharaoh, who said to them: “Go, sacrifice to the Lord your God. Who are they who would go?”
Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
9 Moses said: “We will travel with our little ones and our elderly, with our sons and daughters, with our sheep and herds. For it is a solemnity of the Lord our God.”
Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
10 And Pharaoh responded: “So let the Lord be with you. But if I were to release you and your little ones, who would doubt that you intend some great wickedness?
Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
11 It will not be so. However, go only with the men, and sacrifice to the Lord. For this, too, is what you yourselves requested.” And immediately they were cast out from the sight of Pharaoh.
Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
12 Then the Lord said to Moses: “Extend your hand over the land of Egypt, toward the locusts, so that they may rise up over it, and devour every plant which remains from the hail.”
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
13 And Moses extended his staff over the land of Egypt. And the Lord brought a burning wind all that day and night. And when morning came, the burning wind lifted up the locusts.
Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
14 And they ascended over the entire land of Egypt. And they settled into all the parts of the Egyptians: innumerable, such as had not been before that time, nor ever would be thereafter.
suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
15 And they covered the entire face of the land, laying waste to all things. And the plants of the land were devoured, along with whatever fruits were on the trees, which the hail had left behind. And nothing at all of the greenery remained on the trees or on the plants of the earth in all of Egypt.
Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
16 For this reason, Pharaoh hurriedly called Moses and Aaron, and he said to them: “I have sinned against the Lord your God, and against you.
Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
17 But now, release me from my sin even this time, and petition the Lord your God, so that he may take this death away from me.”
Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
18 And Moses, departing from the sight of Pharaoh, prayed to the Lord.
Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
19 And he caused a very strong wind to blow from the west, and, seizing the locusts, it cast them into the Red Sea. There remained not so much as one in all the parts of Egypt.
Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
20 And the Lord hardened the heart of Pharaoh; neither did he release the sons of Israel.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
21 Then the Lord said to Moses: “Extend your hand into the sky. And let there be a darkness over the land of Egypt, so dense that they may be able to feel it.”
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
22 And Moses extended his hand into the sky. And there came a horrible darkness in the entire land of Egypt for three days.
Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
23 No one saw his brother, nor moved himself out of the place where he was. But wherever the sons of Israel were living, there was light.
Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
24 And Pharaoh called Moses and Aaron, and he said to them: “Go, sacrifice to the Lord. Only let your sheep and herds remain behind. Your little ones may go with you.”
Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
25 Moses said: “You must also permit us victims and holocausts, which we may offer to the Lord our God.
Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
26 All the flocks shall travel with us. Not one hoof of them shall remain behind. For they are necessary for the worship of the Lord our God, especially since we do not know what ought to be immolated, until we arrive at the very place.”
Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
27 But the Lord hardened the heart of Pharaoh, and he was not willing to release them.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
28 And Pharaoh said to Moses: “Withdraw from me, and beware that you no longer see my face. On whatever day you will appear in my sight, you shall die.”
Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
29 Moses responded: “So be it, just as you have said. I will no longer see your face.”
Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”

< Exodus 10 >