< Deuteronomy 18 >

1 “The priests and the Levites, and all who are from the same tribe, shall have no portion or inheritance with the rest of Israel. For they shall eat the sacrifices of the Lord and his oblations.
Firistocin da suke Lawiyawa, tabbatacce dukan kabilar Lawi, ba za su sami rabo ko gādo tare da Isra’ila ba. Za su yi rayuwa a kan hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta ne, gama wannan ne gādonsu.
2 And they shall receive nothing else from the possession of their brothers. For the Lord himself is their inheritance, just as he said to them.
Ba za su sami gādo a cikin’yan’uwansu ba; Ubangiji ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
3 This shall be the recompense for the priests from the people, and from those who offer victims, whether they will immolate an ox or a sheep. They shall give to the priest the shoulder and the breast,
To, ga rabon da jama’a za su ba firistoci daga hadayun da suka miƙa ta bijimi ne, ko ta tunkiya ce; sai su ba firistoci kafaɗar, kumatun, da kuma kayan cikin.
4 the first-fruits of grain, wine, and oil, and a portion of the wool from the shearing of the sheep.
Za ku ba su nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabinku, da manku, da kuma gashi na fari daga askin da kuka yi na tumakinku.
5 For the Lord your God himself has chosen him out of all your tribes, so that he may stand and minister to the name of the Lord, him and his sons, forever.
Gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su da zuriyarsu daga cikin dukan kabilanku don su tsaya su yi hidima a cikin sunan Ubangiji har abada.
6 If a Levite departs from one of the cities, throughout all of Israel, in which he lives, and if he wills and desires to go to the place which the Lord will choose,
Idan Balawe ya tashi daga wani garinku, wurin da yake da zama a Isra’ila, ya tafi a wurin da Ubangiji ya zaɓa, zai iya dawo a duk lokacin da ya ga dama.
7 he shall minister in the name of the Lord his God, as do all his brothers, the Levites, who will be standing at that time in the sight of the Lord.
Zai iya yin hidima a cikin sunan Ubangiji Allahnsa kamar dukan sauran’yan’uwansa Lawiyawa waɗanda suke hidima a can, a gaban Ubangiji.
8 He shall receive the same portion of food as the rest also receive, besides that which is due to him in his own city, by succession from his fathers.
Zai sami rabo daidai da sauran, ko da yake ya karɓi kuɗin mallaka na iyali da ya sayar.
9 When you will have entered into the land which the Lord your God will give to you, be careful that you are not willing to imitate the abominations of those nations.
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku kwaikwayi hanyoyin banƙyama na al’ummai da suke can.
10 Do not let there be found among you one who would purify his son or daughter by leading them through fire, nor one who consults seers, nor one who observes dreams or omens. Do not let there be found among you one who practices the occult,
Kada a sami wani a cikinku da ya miƙa ɗansa, ko’yarsa a wuta, ko a sami mai duba, ko mai maita, ko mai fassara gaibi, ko mai sihiri,
11 nor one who uses spells, nor one who consults demonic spirits, nor a diviner, nor one who seeks the truth from the dead.
ko boka, ko mabiya, ko maye, ko mai sha’ani da matattu.
12 For the Lord abominates all these things. And, because of these wicked ways, he will destroy them at your arrival.
Duk wanda yake yin waɗannan abubuwa, shi abin ƙyama ne ga Ubangiji, saboda waɗannan abubuwa banƙyama ne kuwa Ubangiji Allahnku ya kori waɗancan al’ummai kafin ku.
13 You shall be perfect and without blemish with the Lord your God.
Dole ku zama marasa zargi a gaban Ubangiji Allahnku.
14 These nations, whose land you shall possess, they listen to soothsayers and diviners. But you have been otherwise instructed by the Lord your God.
Al’ummai da za ku kora sukan saurari waɗannan masu maita, ko masu duba. Amma ku, Ubangiji Allahnku bai yarda muku ku yi haka ba.
15 The Lord your God will raise up for you a PROPHET from your nation and from your brothers, similar to me. You shall listen to him,
Ubangiji Allahnku zai tayar muku da wani annabi kamar ni daga cikin’yan’uwanku. Dole ku saurare shi.
16 just as you petitioned of the Lord your God at Horeb, when the assembly was gathered together, and you said: ‘Let me no longer hear the voice of the Lord my God, and let me no longer see this very great fire, lest I die.’
Gama abin da kuka nema daga Ubangiji Allahnku ke nan a Horeb, a ranar taro, sa’ad da kuka ce, “Kada ka bari mu ji muryar Ubangiji Allahnmu, ko mu ƙara ganin wuta mai girma, in ba haka ba, za mu mutu.”
17 And the Lord said to me: ‘They have spoken all these things well.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Abin da suka faɗa yana da kyau.
18 I will raise up a prophet for them, from the midst of their brothers, similar to you. And I will place my words in his mouth, and he will speak to them all the things that I will instruct him.
Zan tayar musu da wani annabi kamar ka daga cikin’yan’uwansu; zan sa kalmomina a cikin bakinsa, zai kuma faɗa musu kome da na umarce shi.
19 But against anyone who is not willing to listen to his words, which he will speak in my name, I will stand forth as the avenger.
Duk wanda bai saurari kalmomina da annabin nan yake magana da sunana ba, ni kaina zan nemi hakki a kan mutumin.
20 But if a prophet, having been corrupted by arrogance, chooses to speak, in my name, things which I did not instruct him to say, or to speak in the name of foreign gods, he shall be put to death.
Amma duk annabin da ya ɗauka cewa yana magana da sunana a kan wani abin da ban umarce shi ya faɗa ba, ko kuwa wani annabin da ya yi magana da sunan waɗansu alloli, dole a kashe shi.”
21 But if, in silent thought, you respond: “How will I be able to recognize a word which the Lord has not spoken?”
Mai yiwuwa ku ce wa kanku, “Yaya za mu san cewa wannan saƙo ba Ubangiji ne ya faɗa ba?”
22 you shall have this sign. If whatever that prophet predicts in the name of the Lord does not happen, then the Lord has not spoken it. Instead, the prophet has formed it through the swelling of his own mind. And for this reason, you shall not fear him.’”
In abin da annabin ya furta da sunan Ubangiji bai faru ba, ko bai zama gaskiya ba, saƙo ne da Ubangiji bai faɗa ba ke nan. Wannan annabi ya yi rashin hankali ne kawai. Kada ku ji tsoronsa.

< Deuteronomy 18 >