< Daniel 3 >

1 King Nebuchadnezzar made a statue of gold, sixty cubits high and six cubits wide, and he set it up in the plain of Dura in the province of Babylon.
Sarki Nebukadnezzar ya yi gunkin zinariya, tsawonsa kamu tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tara ne, ya kafa shi a filin Dura a yankin Babilon.
2 Then king Nebuchadnezzar sent to gather together the governors, magistrates and judges, generals and sovereigns and commanders, and all the leaders of the regions, to come together for the dedication of the statue, which king Nebuchadnezzar had raised.
Sa’an nan ya aika a kira hakimai da wakilai da gwamnoni da mashawarta, da ma’aji, da alƙalai, da marubutan kotu, da dukan sauran ma’aikatan yankunan, suka hallara domin a rusuna wa wannan siffar da ya kafa.
3 Then the governors, magistrates and judges, generals and sovereigns and nobles, who were appointed to power, and all the leaders of the regions were brought together so as to convene for the dedication of the statue, which king Nebuchadnezzar had raised. And so they stood before the statue that king Nebuchadnezzar had set up.
Saboda haka sai hakimai, da wakilai da gwamnoni, mashawarta da ma’aji da alƙalai, da marubutan alƙalai, da kuma dukan ma’aikatan yankunan suka tattaru domin kaddamar da siffar da Nebukadnezzar ya kafa, suka kuma tsaya a gabansa.
4 And a herald proclaimed loudly, “To you it is said, to you peoples, tribes, and languages,
Sai mai shela ya daga murya da ƙarfi ya ce, “Wannan shi ne abin da aka umarce ku ku yi, ya ku mutane da al’umma da kowane yare.
5 that in the hour when you will hear the sound of the trumpet and the pipe and the lute, the harp and the psaltery, and of the symphony and every kind of music, you must fall down and adore the gold statue, which king Nebuchadnezzar has set up.
Da zarar kuka ji karar ƙaho, da sarewa, da garaya da goge da molo da algaita da kowane irin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe ku rusuna ku yi sujada ga wannan gunkin da sarki Nebukadnezzar ya kafa.
6 But if anyone will not bow down and adore, in the same hour he will be cast into a furnace of burning fire.”
Duk wanda bai rusuna ya yi sujada ba, nan take za a jefa shi a cikin tendarun wuta.”
7 After this, therefore, as soon as all the people heard the sound of the trumpet, the pipe and the lute, the harp and the psaltery, and of the symphony and every kind of music, all the peoples, tribes, and languages fell down and adored the gold statue, which king Nebuchadnezzar had set up.
Saboda haka, da zarar suka ji karar ƙaho, da sarewa, garaya da goge da kowane irin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe da kowane irin kaɗe-kaɗe kowane mutum da ko wace al’umma da kowane irin yare suka sunkuya suka yi sujada ga wannan siffa ta zinariya da sarki Nebukadnezzar ya kafa.
8 And soon, about the same time, some influential Chaldeans came and accused the Jews,
A wannan lokaci sai waɗansu masanan taurari suka zo gaba suka yi karar Yahudawa.
9 and they said to king Nebuchadnezzar, “O king, live forever.
Suka ce wa sarki Nebukadnezzar, “Ran sarki yă daɗe,
10 You, O king, have established a decree, so that every man who might hear the sound of the trumpet, the pipe and the lute, the harp and the psaltery, and of the symphony and every kind of music, will prostrate himself and adore the gold statue.
Ya sarki, ka fitar da doka, cewa duk wanda ya ji karar ƙaho, da sarewa, da garayu da goge, da molo da algaita da kowane irin kayan kaɗe-kaɗe da bushe-bushe sai yă rusuna yă yi sujada ga siffar zinariya,
11 But if any man will not fall down and adore, he would be cast into a furnace of burning fire.
kuma cewa duk wanda bai rusuna ya yi sujadar ba za a jefa shi cikin tanderun wuta.
12 Yet there are influential Jews, whom you have appointed over the works of the region of Babylon, Shadrach, Meshach, and Abednego. These men, O king, have scorned your decree. They do not worship your gods, and they do not adore the gold statue which you have raised up.”
Amma sai ga waɗansu Yahudawa waɗanda ka ɗora su a kan harkokin yankin Babilon, wato, Shadrak, Meshak da Abednego waɗanda ba su kula da umarninka ba, ya sarki. Ba su bauta wa allolin ba balle su yi sujada ga gunkin zinariya da ka kafa.”
13 Then Nebuchadnezzar, in fury and in wrath, commanded that Shadrach, Meshach, and Abednego should be brought, and so, without delay, they were brought before the king.
Cikin fushi da hasala, Nebukadnezzar ya aika a kira Shadrak, Meshak da Abednego. Aka kawo waɗannan mutane a gaban sarki,
14 And king Nebuchadnezzar addressed them and said, “Is it true, Shadrach, Meshach, and Abednego, that you do not worship my gods, nor adore the gold statue, which I have set up?
sai Nebukadnezzar ya ce musu, “Gaskiya ne Shadrak, Meshak da Abednego, cewa kun ƙi ku bauta wa alloli kuka kuma ƙi yi sujada ga gunkin da na kafa?
15 Therefore, if you are prepared now, whenever you hear the sound of the trumpet, pipe, lute, harp and psaltery, and of the symphony and every kind of music, prostrate yourselves and adore the statue which I have made. But if you will not adore, in the same hour you will be cast into the furnace of burning fire. And who is the God that will rescue you from my hand?”
Yanzu sa’ad da kuka ji karar ƙaho, da sarewa, da garaya, da goge, da molo da algaita da kowane irin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe, in kuna a shirye ku rusuna ƙasa ku yi wa wannan gunkin da na yi sujada, to, da kyau. Amma in ba ku yi sujada ba, za a je fa ku yanzu a cikin tanderun wutar nan. In ga kowane ne allahn nan da zai kuɓutar da ku daga hannuna?”
16 Shadrach, Meshach, and Abednego answered and said to king Nebuchadnezzar, “It is not right for us to obey you in this matter.
Sai Shadrak, Meshak da Abednego suka amsa wa sarki suka ce, “Ya Nebukadnezzar, ba mu bukata mu kāre kanmu a gabanka a kan wannan batu.
17 For behold our God, whom we worship, is able to rescue us from the oven of burning fire and to free us from your hands, O king.
In an jefa mu cikin tanderun wutar nan, Allahn da muke bauta wa zai iya cetonmu daga ita, kuma ya sarki, zai cece mu daga hannunka.
18 But even if he will not, let it be known to you, O king, that we will not worship your gods, nor adore the gold statue, which you have raised up.”
Amma ko da bai cece mu ba, muna so ka sani, ya sarki; cewa ba za mu bauta wa allolinka ba ko kuma mu yi sujada ga gunkin zinariyar da ka kafa ba.”
19 Then Nebuchadnezzar was filled with fury and the appearance of his face was changed against Shadrach, Meshach, and Abednego, and he commanded that the furnace should be heated to seven times its usual fire.
Sai Nebukadnezzar ya husata da Shadrak, Meshak da Abednego, sai al’amuransa a kansu ya canja. Sai ya umarta a ƙara zuga wutar har sau bakwai domin tă yi zafi fiye da yadda take a dā.
20 And he ordered the strongest men of his army to bind the feet of Shadrach, Meshach, and Abednego, and to cast them into the furnace of burning fire.
Kuma ya umarci waɗansu ƙarfafan sojoji a cikin rundunarsa su daure Shadrak, Meshak da Abednego su jefa su cikin tanderun wutar.
21 And immediately these men were bound, and along with their coats, and their hats, and their shoes, and their garments, were cast into the middle of the furnace of burning fire.
Waɗannan mutanen suna sanye da riguna, da wanduna, da rawani da waɗansu kayan sawa, aka daure su, aka jefa su cikin tanderun wuta.
22 But the king’s order was so urgent that the furnace was heated excessively. As a result, those men who had cast in Shadrach, Meshach, and Abednego, were killed by the flame of the fire.
Sarki ya ba da umarnin da gaggawa kuma wutar ta yi zafi ƙwarai har harshen wutar ya kashe sojojin nan da suka ɗauki Shadrak, Meshak da Abednego,
23 But these three men, that is, Shadrach, Meshach, and Abednego, having been bound, fell down in the middle of the oven of burning fire.
waɗannan mutane uku kuma a daure, suka fāɗa cikin tanderun wutar.
24 Then king Nebuchadnezzar was astonished, and he quickly got up and said to his nobles: “Did we not cast three men shackled into the midst of the fire?” Answering the king, they said, “True, O king.”
Sai Sarki Nebukadnezzar ya miƙe tsaye, cike da mamaki ya tambayi mashawartansa, “Shin ba mutum uku ba ne muka daure muka jefa cikin wutar?” Suka amsa, “Tabbatacce haka yake ya sarki.”
25 He answered and said, “Behold, I see four men unbound and walking in the midst of the fire, and no harm is in them, and the appearance of the fourth is like a son of God.”
Sai ya ce, “Ku duba ina ganin mutum huɗu suna tafiya suna yawo a cikin wutar, a sake kuma babu abin da ya same su, na huɗun sai ka ce ɗan alloli.”
26 Then Nebuchadnezzar approached the entrance of the furnace of burning fire, and he said, “Shadrach, Meshach, and Abednego, servants of the supreme God, come out and approach.” And immediately Shadrach, Meshach, and Abednego went out from the midst of the fire.
Sai Nebukadnezzar ya matsa kusa da ƙofar tanderun wutar ya yi kira da ƙarfi, “Shedrak, Meshak da Abednego, bayin Allah Mafi Ɗaukaka ku fito! Ku zo nan!” Sai Shadrak, Meshak da Abednego suka fita daga cikin wutar,
27 And when the governors, and the magistrates, and the judges, and the powerful of the king had gathered together, they considered these men because the fire had no power against their bodies, and not a hair of their head had been scorched, and their pants had not been affected, and the smell of the fire had not passed onto them.
Sa’an nan hakimai, da wakilai, da gwamnoni da masu ba wa sarki shawara suka kewaya su. Suka ga wutar ba tă yi musu wani lahani a jikinsu ba, babu ko gashin kansu da ya ƙuna; ko warin wuta ma ba su yi ba.
28 Then Nebuchadnezzar, bursting out, said, “Blessed is their God, the God of Shadrach, Meshach, and Abednego, who sent his angel and rescued his servants who believed in him. And they altered the verdict of the king, and they delivered up their bodies, so that they would not serve or adore any god except their God.
Sa’an nan Nebukadnezzar ya ce, “Yabo ya tabbata ga Allahn Shadrak, Meshak da Abednego wanda ya aiko da mala’ikansa ya ceci bayinsa da suka dogara matuƙa a gare shi, suka ki bin umarnin sarki kuma su na a shirye domin su ba da ransu da suka ƙi bauta ko su yi sujada ga wani allah sai dai Allahnsu.
29 Therefore, this decree is established by me: that every people, tribe, and language, whenever they have spoken blasphemy against the God of Shadrach, Meshach, and Abednego, will perish and their homes will be destroyed. For there is no other God who is able to save in this way.”
Domin haka ina ba da doka cewa duk mutane da kowace al’umma ko kowane yaren da ya ce wani abu mummuna a kan Allahn Shadrak, Meshak da Abednego za a yanka shi gunduwa-gunduwa kuma gidansu zai zama wurin zuba shara, domin babu wani allahn da zai iya ceto ta irin wannan hanya.”
30 Then the king promoted Shadrach, Meshach, and Abednego in the province of Babylon.
Sa’an nan sarki ya ƙara wa su Shadrak, Meshak da Abednego girma a yankin Babilon.

< Daniel 3 >