< Amos 6 >

1 Woe to you who have been wealthy in Zion, and to you who have confidence in the mountain of Samaria: aristocrats, heads of the people, who advance with a retinue into the house of Israel.
Taku ta ƙare, ku da kuke zaman sakewa a Sihiyona, da ku waɗanda kuke ji zama a Dutsen Samariya lafiya ne, ku manyan mutanen ƙasar da take sananniya, waɗanda mutanen Isra’ila suke zuwa!
2 Cross over to Calneh and see, and go from there into Hamath the great, and descend into Gath of the Philistines, and to the best kingdoms of these, if their limits are wider than your limits.
Ku je Kalne ku dube ta; ku wuce daga can zuwa Hamat-rabba, sa’an nan ku gangara zuwa Gat a Filistiya. Sun fi masarautunku biyu ne? Ƙasarsu ta fi taku girma?
3 You have been set aside for the day of disaster, and you approach the throne of iniquity.
Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan muguwar rana kuna kuma jawo mulkin tashin hankali kusa.
4 You sleep on beds of ivory, and you are lustful on your couches. You devour lambs from the flock and calves from the midst of the herd.
Kuna kwanciya a kan gadajen da aka yi musu shimfiɗar hauren giwa kuna mimmiƙe a kan kujerunku. Kuna cin naman ƙibabbun raguna da na ƙosassun’yan maruƙa.
5 You sing to the sound of stringed instruments; they consider themselves to have the musical abilities of David.
Kuna kaɗa molayenku yadda Dawuda ya yi kuna ƙirƙiro waƙoƙi a kan kayan kaɗe-kaɗe.
6 You drink wine in bowls, and you anoint with the best ointments; and they suffer nothing over the grief of Joseph.
Da manyan kwanoni kuke shan ruwan inabi kuna kuma shafa mai mafi kyau, amma ba kwa baƙin ciki game da kangon da Yusuf ya zama.
7 Because of this, now they will depart at the head of those who go into captivity; and the faction of the lustful will be removed.
Saboda haka za ku zama na farkon da za su tafi zaman bauta; bukukkuwanku da shagulgulanku za su ƙare.
8 The Lord God has sworn by his own soul, the Lord God of hosts says: I detest the arrogance of Jacob, and I hate his houses, and I will hand over the city with its inhabitants.
Ubangiji Mai Iko Duka da kansa ya rantse, Ubangiji Allah Maɗaukaki ya furta, “Ina ƙyamar girman kan Yaƙub, ba na kuma son kagarunsa; zan ba da birnin da duk abin da yake cikinta.”
9 For if there were ten men remaining in one house, even they will die.
Ko da mutum goma ne suka ragu a gida guda, su ma za su mutu.
10 And his closest relative will steal him away and will burn him, so that he may carry the bones out of the house. And he will say to him that is in the inner most rooms of the house, “Now is there any left that still belongs to you?” And he will answer, “It is finished.” And he will say to him, “Be silent and do not call to mind the name of the Lord.”
In kuma wani dangi ya shiga don yă fitar da gawawwakin yă ƙone ya kuwa tambayi wani wanda yake ɓoye a can, yana cewa, “Akwai wani tare da kai?” Ya kuwa ce, “Babu,” sai yă ce, “Kul! Kada mu ambaci sunan Ubangiji.”
11 For behold, the Lord has commanded, and he will strike the greater house with catastrophes, and the lesser house with divisions.
Gama Ubangiji ya ba da umarni, zai kuma ragargaza babban gidan nan kucu-kucu ƙaramin gidan kuwa zai yi rugu-rugu da shi.
12 Can horses gallop across rocks, or is anyone able to plough with gazelles? For you have turned judgment into bitterness and the fruit of justice into wormwood.
Dawakai sukan yi gudu a kan duwatsu? Wani yana iya yin noma a teku da shanun noma? Amma ga shi kun mai da gaskiya ta zama dafi amfanin adalci kuma ya zama ɗaci,
13 You rejoice in emptiness. You say, “Have we not, by our own strength, taken horns for ourselves?”
ku da kuke murna saboda an ci Lo Debar da yaƙi kuka kuma ce, “Ba da ƙarfinmu ne muka ƙwace Karnayim ba?”
14 For behold, house of Israel, I will raise up a people over you, says the Lord God of hosts, and they will crush you from the entrance of Hamath all the way to the burning of the desert.
Gama Ubangiji Allah Maɗaukaki ya ce, “Zan sa wata ƙasa ta tayar muku, ya ku gidan Isra’ila, wadda za tă matsa muku tun daga Lebo Hamat zuwa kwarin Araba.”

< Amos 6 >